Posts

Showing posts from July, 2014

barkan muda sallah

ayi wankan sallah asa wani katan bakin gilas kamar me walda sai yan matan #‎ADAMAWA‬ ayi wankan sallah a shafa wani jan jabaki sai yan matan #‎SOKOTO‬ ayi wankan sallah a dau talan rogo sai yan matan #‎ZARIA‬ anaso ayi kwalliya amma ba'aiyaba sai yan matan #‎KADUNA‬ anaso akwaikwayi wankan wasu garuruwan amma ba'aiyba sai yan matan #‎JIGAWA‬ ga kudi gasa kaya masu tsada da daukar wanka amma ba samari sai yan matan #‎ABUJA‬ ayi wanka iya wanka asa silifas sai yan matan #‎KATSINA‬ ayi wankan sallah afito ana siyan gurasa sai yan matan #‎NASARAWA‬ ayi wanka asa kaya afito ana kallan jiki sai yan matan #‎BAUCHI‬ (abinka da basabunba) ayi wanka ai ta zagaya titi sai yan matan #‎GOMBE‬ ayi wanka asaka pensil a dinga tafiya kamar maza sai yan matan #‎JOS‬ ga kyau ga iya daukar wanka da jan hakalin samari sai yan matan #‎KANON_DABO‬ Ayi wanka ashafa kur-kur sai yan matan #‎TARABA‬

tsuntsu da annabi musa

Wata rana Annabi Musa yana zaune sai yaga wani tsuntsu mai kyawun gaske ya shiga cikin tabo sai jikinsa ya baci ya koma yayi muni, sai tsuntsun ya shiga cikin ruwa ya wanke jikinsa sai kyawunsa ya dawo. yayi tayin haka har sau biyar, sai mamaki ya kama Annabi Musa, yace Allah kasa sanar dani fassarar abinda wannan tsuntsu ya aikata, sai Allah ya sanar dashi cewa kamar haka al'ummar Annabi muhammadu zasu dinga aikata zunubi amma da zarar sunyi sallah ta farilla to wannan zunubi ya goge kamar yadda wannan tsuntsu yake wanke jikinsa. Allah yasa mu dace....

maza ina kuke

Bayani akan gyaran al'auran namiji mafiyawan yan uwana maza suna fama da matsala azakari zakaga takoma kankani kamar nakaramin yaro. Ga duk wace ke son taimakawa mijin ta, ko ga duk mai son magani kahada dakanka kana iya hadawa da kanka. . Yadda zakahada magani Zakasamo wani ganye yana nan bayn gari anakiran ganyen (hankufa) Sai kashanya hankufa natsawo kwana 2 a rana sai kadaga hankufan bayan yabushe sai ka tankade kaxuba ga lade ka ajiya. Saikasamu nonon-shano ko madara sai kaxuba hankufan so uku a cikin madara ko nono sai kasamu zuma fara kahada kasamu kwana 7 kanasha insha allah zakaga takara tsawo da girma kuma zakasamu karin lafiya a jikinka. Nayi hakan ne badun azageni saboda taimakama yan uwana musulumai wannan abu bakuma nayi bane dun batanci wanda yaga xai iya gwada ya jaraba yagani insha allah xaisamu lapiyan haka.

topa

HATTARA DAI JAMA'A MUSULMAI MUTANEN AREWA!!! Yanzun nake shirin kwanciya sai na leqa Whatsapp domin sada zumunci kafin na kwanta sai wata 'yar uwa ta turo wannan saqon ta group. Saqon ya girgizani kuma dama duk wani mai kaifin hankali yakamata ma ace dama yafara zargin hakan kamar yadda naga wani yayana TABARI YERO yayi wannan maganar ta cewa, shifa yana bada shawarar adena tunanin neman 'yan matan nan, domin kuwa su jonathan ne suka sacesu kuma suka tsafancesu shine sukayi training dinsu suka koyamusu harbi da kuma dasa bomb. To ilai kuwa sai naci karo da wannan saqon na 'yar uwa, ga sakon nata kamar haka. "Akwai keke napep danataba shiga wlh mutumin yaban tsoro. Yace tunda ni musulmace zai daure yagayamin wata magana. Cewa yayi yaran da aka sace bawai nemansune baayiba. Training dinsu akeyi ana koya musu harbi da saka bomb. Harda cewa wlh musammam mu mata dazamuyi baki agida mufara zumunci. A kiyaye bako koda dan uwan mijinki ne bakisaniba kibari mijin yatantance...

another bornanza

haba jama'a, wai shin menene kesa bamu zurfafa tunaninmu, da kuma yin amfani da hankalinmu? har idan kamfanin Globacom zata kawo mana bonanza na idan kasa kudi zata baka garabasan fiye da kudin da kasa, har kaga muna tururuwan sa kudi kullum..... har idan kamfanin ETISALAT zasuke baku kyautan 15MB duk sati idan kunsa naira dari biyu......kai wani ma ko ana ha maza ha mata sai ya nemi kudi.....don more wannan garabasan!! to amma gashi an umurcemu dayin azumi shida a wannan wata na shawwal amatsayin BONANZA wanda yake rubanya lada da bamu garabasan samun falalan azumin wata biyu...wanda idan ka hada da azumin Ramadan da mukayi, muna sa ran samun falalan wanda ya shekara yana azumi.......amma mafiyawancinmu bamu bada hakan mahimmanci...... jama'a ina mana NASIHA har idan MTN da shauransu zasu ja hankulanmu, mai zai hana mufi karkata wajen samun rahaman ubangijinmu, muyi kokari mu ribaci wannan azumi na sitta shawwal.......

free browsing

mtn free browsing !!!!!!!!!!!!!!-------!!!!!!!!!! 1...Dial 662 6#. select 1, send...and select 3, send... to subscribe for the plan you see there (monthly trial). You get 100mb for trial free. 2. Use your m t n default settings for java, symbian and android users. 3. Open any of your handler apps (ucbrowser, opera, etc) and set this: Proxy Type: Real Host Proxy Server: jumia.com.ng or jumia.com !!!!!!!!!!!!!!-------!!!!!!!!

ya jibgi mahaifiyar sa

YA DUKI MAHAIFIYARSA Bisa tsare tsarensa na kowace rana sai ya duki matarsa tare da hujjah koh babu. Lamarin dake 6ata ran mahaifiyarsa matuka. Kasancewarsa daa ga limamin garin, hakan yasa iyayen matarsa ke matukar jin nauyin gidansu. A duk lokacin da ta kawo korafi gida, cikin rarrashi ake lalla6arta ta koma tare da nuna mata cewa xa'a samu sauyi nan bada jimawa ba. #Lado mashayi ne, kuma bai juma ba da Mahaifinsa ya rasu a sakamakon matsananciyar ciwon xuciya wanda ya gamu da ita a dalilin dansa Lado. Rannan cikin dare, bayan Lado ya dawo daga yawace yawacensa kamar yadda ya saba har kullum. Ya tarar da mahaifiyarsa tare da matarsa cikin daki guda suna phira har suna shewa. Ran Lado yayi matukar 6aci da abinda ya tarar, a cewarsa, Uwarsa ce take bawa matarsa muggan shawarwari. Don haka nan take ya hau mahaifiyar tasa da duka, ihu matar ta ringa yi amma babu wanda ya kawo musu dauki. Da kyar uwar ta samu ta rarrafa ta bar gidan sannan ta sha. Irin wadannan 'ya'ya Allah ka...

ebola virus

Things you need to know about Ebola Virus to stay SAFE… 1. It is a Central African disease that has traveled over countries in a living host to West Africa. It is easily spread by physical contact and eating contaminated bush meat. Major hosts are in 5 species of Bats but monkeys and apes are easily infected and killed. 2. It kills in a week, leaving no time to treat an individual. 3. It has no known vaccine or cure 4. Known cases have been experienced recently in Guniea, Liberia and Central Africa Rep, spreading eastwards and westwards towards Nigeria. Death toll so far in West Africa is over 100. 5. The Ebola outbreak of 2014 is the most challenging one witnessed in Africa. What we can do? 1. Avoid eating any bush meat for now! Especially Apes and Bats. 2. Wash your hands as regularly as possible, especially after shaking a stranger. It is spread by contact. 3.The most straightforward prevention method during Ebola outbreaks is not touching patients, their excretions, and body fluids...

hahahah

Wata yarinya ce tayi cikin shege, daya fara girma sai iyayenta suka tambayeta wanda yayi mata cikin, sai ta fadi wani attajiri makwabcin sune , Sai uban yaja yarinyar da mahaifiyarta suka dunguma xuwa gidan attajirin Suna xuwa gidan suka tarar da Alhaji suka shaida masa halin da ake ciki , sai attajirin yace ya kar6i ciki amma da sharadi guda 3:- "Idan yarinya ta haifi namiji xai ba uban yarinya naira million 10 yaba uwar million 5 , Idan kuma ta haifi mace xaiba uwar yarinyar million 10 yaba mahaifinta 5 , Idan kuma har cikin ya xube shikenan kowa ya rasa , sai uban yarinyar yayi murmushi yace "haba Alhaji ai saika mata wani cikin ko kuwa uwar gida ? Sai uwar gida tace kwarai kuwa hakane saina basu dakina ma

mafusata

Mafusata Sun Yi Wa Sheik Yusuf Sambo Ya Sha Duka A Kaduna Daga Ibrahim Ammani, Kaduna Daruruwan wasu fusatattun matasa ne suka yi kukan kura, inda suka afkawa mataimakin shugaban majalisar malamai ta kasa, na kungiyar Izala, Sheik Yusuf Sambo Rigachikum, a yayin da ya halarci wajen rufe Tafsirin Al kur'ani mai girma wanda Dakta Ahmad Gumi, ke gabatarwa a masallacin Sulatan Bello da ke Kaduna. Kamar yadda Mallam Yusuf Sambo ya saba, yakan halarci karatun Tafsirin Kur'anin gabatarwa Dakta Gumi, a kowace rana da yammaci, saidai a ranar rufe tafsirin kwana guda bayan tashin tagwayen bama bamai da akayi a Kaduna, Malamin na shigowa, matasan wadanda kamar suna jiranshi suka afka mishi. Matasan sun rinka fadin cewa, Allah ya isa munafukin Malami, malamin Jonathan, a miko manashi mu aske gemunshi. Lamarin daya sanya dole jami'an tsaro suka shigo cikin masallacin domin magance al'amarin, kafin nan tuni wasu matasa har sun fara kai mishi duka gami da keta tufafin dake jikinshi. D...

hukunci

MENENE HUKUNCIN WANDA YACI ABINCI KO YASHA RUWA ABISA MANTUWA ALHALI YANA AZUMIN RAMADAN ??? AMSA ----- Sai yaci gaba da azuminsa yana nan bai karye ba, domin Allah ne yaciyar dashi ya shayar dashi. Daili kuwa ya tabbata daga Abi Hurairata (R.A) daga Manzon Allah (S.A.W) yace: "Idan mutum ya manta, yaci ko yasha, to sai yaci gaba da azuminsa, domin Allah ne ya ciyar dashi ya shayar dashi. _ ___________________________________ Kuduba Attarghib wattarhib na munzuri lahakikin sheikh Albany Juzu'I na farko shafi na (2). Suratul Baqarah, ayata183. Sahihul Bukhari hadisi mai lamba ta (1933). Dan Allah kuyi Like da share dinsa saboda yan uwanku su amfana. Allah ya hadamu acikin ladan baki daya.

allah. mai iko

ALLAHU AKBAR !!! ••• ANGA WATA HALITTA IRINTA DAN ADAM, AMMA KUMA ALULLUBE DA HASKE ACIKIN MASALLACIN ANNABI (s.a.w)••• A ranar juma'ar data wucene acikin masallacin ANNABI (s.a.w) dake agarin MADINA kasar saudiyya, Wata CAMERA ta cikin masallacin tadauko hoton wani bawan Allah, me siffa irin ta mutane amma kuma lullube yake da HASKE daga fuskarshi har tufafinshi. Bayan an idar da sallah lokaci me tsawo, sai labarin yafara shiga INTERNET (youtube), aka tambayi shugaban masallacin AS- SHEIKH ABDULWAHID HUTTAB sai yace : Mu bamuga komaiba alokacin da ake cikin hudubar Jumu'ah, sedai munga CAMERAR MASALLACI ta watsa bayani a INTERNET se nagani. Kuma ankara tambayar wani malami a tsangayar AL'AMRU BIL MA'RUF WAN NAHYU ANIL MUNKAR, a JAMI'AR MUSULUNCI dake MADINA, mai suna : AS-SHEIKH DR. GHAZY ALMUTAYYARI dangane da fadin mutane da suke cewa : wannan halittar bata DAN ADAm bace, sai yace: " Lallaikam wannan lamari yana cikin abubuwan gaibu wanda ba'ayimusu shis...

dalilin rikicin zirin gaza

DALILIN RIKICIN GAZA (PART 1) * ****************************** HITLER YACE; Ragowar YAHUDAWAN da na bari a raye a duniya, na barsune domin mutane su tambatar da makircinsu, su tambatar da basuda amfani a duniya. HITLER»» Dai wani sojane da ya kashe yahudawa ba adadi, wannan dalilin yasa yahudawa suka watsu a cikin duniya suka bar kasarsu suka rasa muhalli, bayan mutuwarsa ne turawa ke kokarin sama masu kasar da zasu zauna, shine sukace GAZA tasuce shine musabbabin yaki tsakanin Palasdin da Isra'il akan ZIRIN GAZA. ZIRIN GAZA dai yankine ko kasace ta Palasdin, Palasdin kuma kasace ta musulmai. ISRA'IL kuwa kasace ta Yahudawa makiya musulunci da musulmai, wanda a kwanannan su kace sai sun kashe musulman Palasdin ga baki daya, har yanzu kashe musulmai suke yara da manya, hari ta sama da kasa. ZAMUYI ADDU'A DAN ALLAH RUBUTA MANA....(AMEEN A COMMENT) YA ALLAH ALBARKACIN WANNAN WATA DA MUKE CIKI YA ALLAH KA TAIMAKI MUSULMI DA MUSULMAI A DUK IN DA SUKE, YA ALLAH KA KASKANTA KAFIRC...

MUHAMMAD BN ABDULLAH (Sallallahu alaihi wasallam)!!!!!

MUHAMMAD BN ABDULLAH (Sallallahu alaihi wasallam)!!!!! Sunansa: MUHAMMAD SAW. Sunan Mahaifinsa:ABDULLAH. Sunan Mahaifiyarsa:AAMINAH. An haifeshi (saw): 12/rabi'ul awwal/shekarar giwa. Wajen haihuwarsa (saw):MAKKAH. Yai Rayuwarsa (saw):MAKKA DA MADEENA.. Aikinsa(saw): KIWO,KASUWANCI,ANNABTA,CIKA MAKIN ANNABAWA DA MANZANNI... Matansa (saw) -NANA KHADIJAH(ra) -SAUDAH BNT ZAMAH(ra) -AISHA BNT SADDEEQ(ra) -HAFSAH BNT UMAR(ra) -UM SALAMAH(ra) -JUWAIRIYYAH BNT HARITH (ra) -UM HABEEBA (ra) -ZAINAB BNT JAHSH (ra) -SAFIYYAH BNT HUYAIY (ra) -ZAINAB BNT KHUZAIMAH (ra) -MAIMUNAH BNT HARITH (ra) -MARIYYAH ALQIBDIYYAH (ra) YA'yansa (saw): -IBRAHIM -ALQASIM -ABDULLAH -ZAINAB -RUQAYYAH -UM KULTHUM -FAATIMAH Wafatinsa (rasuwarsa) (saw): 12/Rbi'ul awwal/11h Shekarunsa (saw): 63 Wanda sukai masa wanka (saw): -ALIYU BN ABY TAALIB(ra) -ABBAS BN ABDULMUDDALIB(ra) -FADL DA QATHM IBNAA ABBAS.. -USAAMAH BN ZAID DA SHAQRAAN..(masuyi masa hidima) -Abbas bn Abdulmuddalib yana juya jikinsa me tsarki(SAW...

muna rokon allah baya amsawa

MU NA ROKON ALLAH BA YA AMSAWA?. Wata rana Ibrahim bin adham ya gifta ta cikin kasuwar basara, sai mutane suka ce masa "ya aba ishaq, muna roqon Allah baya amsawa, sai yace" qila zukatanku sun qeqashe akan abubuwa goma" 1. kun san Allah amma bakwa bashi haqqoqinsa, 2. kuna riya son manzonsa amma bakwa aikata sunnarsa, 3. kuna karanta Qur'ani amma bakwa aiki da shi, 4. kuna cikin ni'imar Allah amma bakwa godewa, 5. kuna cewa shaidan maqiyin Allah ne amma bakwa sa6a masa, 6. kuna cewa Aljannah gaskiya ce amma bakwa aiki da zai kai ku cikinta, 7. kuna cewa wuta gaskiya ce amma bakwa guje mata, 8. kuna cewa mutuwa gaskiya ce amma bakwa shirya mata, 9. kuna rufe matattun ku amma bakwa wa'azzantuwa, 10. kuna ta barcin ku kwananku yana qarewa amma kuna ta shagaltuwa akan aibanta wasu kuna manta aibinku. YA ALLAH KA AMSA ADDU'O'IN MU NA ALHERI BA DON AYYUKAN MU BA.

s a w

WANI SAHABI YA SHIGO MADINAH BAYAN WAFATIN MANZON ALLAH (S.A.W) SAI GUZURINSA YAQARE YAYI 'YAN KWANAKI BAI SAMU ABINCI BA. SAI YAJE RAUDHAR MANZON ALLAH (S.A.W) YACE:- "YA RASULULLAHI NI BAQONKA NE NAMIQA LAMURA NA GAREKA" SAI BARCI YAKWASHE WANNAN BAWAN ALLAH. KAWAI SAI YAYI MAFARKI ANNABI (S.A.W) YABASHI GURASA, YACI RABI, KODA YA FARKA SAI YAGA SAURAN RABIN A HANNUNSA. SALLALLAHU ALAIHI WA SALLAAM! (Mai Neman Karin Bayani Ya Duba Littafin: Tafsirul- Ahlam Na Muhammad Bin Sirina Babin Da Yake Magana Akan Mafarki Da ANNABI (Alaihis Salatu Wassalam), YA ALLAH! KA BARMU DA SOYAYYAR SAYYIDUL- WUJUDI (S.A.W) DUK RINTSI DUK WUYA.

ladduba

WASU DAGA CIKIN LADUBAN DA SUKA SHAFI RANAR IDI 1. Yin wanka- Sa'id dan Jubair, yana cewa : "Abubuwa uku, sunnoni ne na idi : tafiya a kasa, da yin wanka, da cin abinci kafin a fita" 2. Cin abinci kafin a fita- An karbo daga Anas dan Malik ya ce : "Manzon Allah s.a.w. ba ya fita idin karamar sallah har sai ya ci dabinai kafin ya fita" 3. Yin kabbara ranar idi- wannan yana daga cikin manyan sunnonin ranar idi. Lokacin fara kabbara a idin karamar sallah shi ne : daren idi har zuwan liman ya shiga sallar idi. 4. Siffar kabbara- An karbo daga Ibnu Mas'ud -Allah ya yarda da shi – ya kasance yana kabbara a ranakun sha daya da sha biyu da sha uku na watan hajji, yana cewa : Allahu Akbar, la'ilaaha, illallah, wallahu akbar, Allahu Akbar, wa lillahil hamd" 5. Yiwa juna fatan alkairi (barka da sallah) An karbo daga Jubair dan Nufair ya ce : "Sahabban Annabi s.a.w. sun kasance idan sun hadu da juna ranar idi sashinsu yana cewa sashi : Allah ya karbi ibadu...

baffula tani

Wani bafulatani neh zashi kasar waje bayan sun shiga jirgi an fara tafiya sai akayi announcing za a raba abinci kowa sai ya fadi abunda yakeso a kawo masa , a wannan lokacin akwai wani bature a gefen fillo shi kuma fillo a ranshi saiya yanke shawarar shima yau duk kalan abincin da bature zaici to shima sai yaci Pullo ya kasa kunne yana jira yaji sunan kalar abincin da bature zai fada sai akazo gun bature aka tambaye shi wanne kalar abinci yakeso sai yace NOTHING aka wuce akazo gun fillo shima aka tambaye shime yakeso akawo masa shima yace NOTHING aka wuce shi, shiru shiru pullo yaji ba ace masa komai ba , Bayan minti talatin 30 fillo yaji dai yunwa ta dame shi sai ya tashi a fusace yaje gun masu bada abinci yace" kai dan uwa aradu koma wane irin abinci ne abani a kyale NOTHING din nan na fasa abanikoda kosai ne

**IDAN KAINE YAYA ZAKAYI?**

0**IDAN KAINE YAYA ZAKAYI?** Wani alhajine yaje kauyensu ziyara da motarsa, to a hanyar dawowa sai dare yamasa, yana cikin tafiyane sai yahango wani mutum gefen titi. Sai yatsaya , sai mutumin yace alhaji ataimaka a ragemin hanya zuwa cikin gari mana. Sai alhaji yace bamatsala shigo mutafi..... Suna cikin tafiya sai alhaji yahango kofato a kafar wannan bawan allah, ,,,,,, sai alhaji yakashe motar.... Sai yacewa wannnan mutumin dan fita katuromu motar ta mutu..... Sai mutumi yafita yana cikin tura motane sai kawai alhaji yayi mota key yagudu..... Yana cikin tsala uban gudune yayi tafiyar kilometer wajen 50..... Sai kawai wannan mutumin ya leko ta window yace :: alhaji har yanzu motar bata tashi bane????????

inkai ne yaza kai

IDAN KAINE YAYA ZAKAYI? Wani alhajine yaje kauyensu ziyara da motarsa, to a hanyar dawowa sai dare yamasa, yana cikin tafiyane sai yahango wani mutum gefen titi. Sai yatsaya , sai mutumin yace alhaji ataimaka a ragemin hanya zuwa cikin gari mana. Sai alhaji yace bamatsala shigo mutafi..... Suna cikin tafiya sai alhaji yahango kofato a kafar wannan bawan allah, ,,,,,, sai alhaji yakashe motar.... Sai yacewa wannnan mutumin dan fita katuromu motar ta mutu..... Sai mutumi yafita yana cikin tura motane sai kawai alhaji yayi mota key yagudu..... Yana cikin tsala uban gudune yayi tafiyar kilometer wajen 50..... Sai kawai wannan mutumin ya leko ta window yace :: alhaji har yanzu motar bata tashi bane???????

wasa kwakwalwa

****{WASA KWAKWALWA}**** Wani mutumne yanada 'ya''ya guda uku. Wata rana yana cin dambu tareda ''ya''yan nasa sai yashake sai yace da babbansu yatashi yadebo masa ruwa sai yace bazashiba sai yaceda kaninsa tunda yayanka yaki zuwa to kai debomin shikuma sai yace masa jira mugama cin abincin. Shikuma karamin cikinsu sai yacewa uban nasu kaima baba karabu dasu kaje kashawo ruwanka amma idan kasha kataho mini dashi DAGA CIKINSU WAYE YAFI RASHIN KUNYA {wassalam}

AYYUKA GUDA 10 LADANSU DAI DAI DA QIYAMUL-LAILI!

AYYUKA GUDA 10 LADANSU DAI DAI DA QIYAMUL-LAILI! Mu ji tsoron ALLAH kuma mu binciki kanmu domin tafiya zuwa barzahu zuwa lahira yana nan kusa don haka mu yi tattali. Mu yi aiki na kwarai domin ALLAH yana kallonmu. Hakika Magabata na kwarai ba sa wasa da KIYAMULLAILI domin guzurinsu zuwa Lahira. Saboda kaunar da ALLAH yake mana tare da tausaya mana, sai yayi mana kyautan wasu ayyuka masu sauki wanda idan aka yi su za'a sami ladan kiyamullaili, idan kai ragone baka KIYAMULLAILI to kada wadannan ko wasu bangarensu su subuce maka, idan kuma kana KIYAMULLAILIN ka hada da wadannan rayuwarka zai yi albarka da yawan lada, kada in cikaku da surutu ga su nan kamar haka: 1-KARANTA AYOYI 100 A DARE: ANNABI (SAW) yace: "Wanda ya karanta ayoyi 100 da dare za'a rubuta masa ladan kiyamullaili". [AHMD, DRM-3450, SHH-JM'U-6468]. 2-KARANTA AYOYI 2 NA KARSHEN BAQARA: "Wanda ya karanta ayoyi biyun karshen Baqara da dare to ya ishe a matsayin kiyamullaili da kariya." [AHMD, B...

aku da matar uban gidansa

                       AKU DA MATAR UBAN GIDANSA Wata rana wani attajiri za shi fatauci sai ya bar matarsa agida yana da wani aku. Sunnan tare sai matar ta rika fita yawao don taga mijin bayanan. Barorin gida da suka ga abin damesu   basu da dammar yin Magana kada matar nan ta sare su wajen mai gida in ya komo. Saboda haka suka zura ido   Ana nan ran nan sai maigida ya dawo . kasan a;la amrin doniya bashi boyuwa , sai wani tsegunta masa abin da matarsa tayi ta aikatawa bayan bashi nan yaji haka, sai ya kiar matar ,yasameta yayi ta zagi. Ya dauki   sanda kuma yabata kasha. Da matanan nan taga haka sai tayi yaji , aka koma da ita. Tace a ranta , “ Ba wanda ya fadi   sai aku “   kasan mu , Allah yabaka nasara , bakin   jini   garemu kwarai , tum ba game da mataba. Suna cewa mu fiya tsegumi . Saboda haka , ta bari mai gida ya tafi kasuwa , sai takama aku, tafige shi da rai ,ta wurga shi waje ta taga , tace, “ daga gareni kabar Tsegumi “ Allah yasa aku bai mutuba , ya tsallaka har   ...

dan fulani

Yan fullani da abinci. Wasu fulani ne. Su hudu. sunje bakunta. Wani gari. Da zuwansu aka basu masauki mai kyau aka karramasu sosai Ana shirin akawo musu abinci domin suna jin yunwa. Sosai kuma gaya lokacin sallah yayi sai sukace su suna kara'I baza suje massalaci ba. Sai aka kawo musu ruwa abuta. Suka fara alwalla. Da suka. Gama Sai suka fara sallah. Fara sallar su ke dawuya sai aka kawo abincin. Sai daya. Yace lahh an kawo abinci sai na kusa dashi Yace kai in anna sallah ba'a magana. Sai na ukun yace Kaga dani da limanne kawai Ba muyi magana ba. Can sai Gogan naka yace. Akafada muku ni wawa ne da zan kula ku. Hahah ragas.

NASHA WAHALAR SOYAYYA. kashi na 5

KARSHEN LABARIN. ---------------------------------- DAMA... DAMA... HAJARA takasa karasa abinda takeson fadi nakatseta kinga hajara dan allah inkinsan bakida abin fadi kikyaleni ni ina cikin farin cikina karki batamin rai inagama fadin hakan nakashe wayar naturar da ita gefe tareda jan wani dogon tsaki, inacikin farincikina zakizo kibatamin rai, ko second goma ba akaraba tasake kira nadaga dan Allah dan annabi hajara karki sake kiran wayanan wai maikike nufi danine nace miki kikyaleni inkuma yauma wulakancin zakimin to wlh barina fadamiki allah bazan jureba sai na rama. Muryarta narawa tace idress wlh ba wulakanci zanmakaba nakirakane dama nabaka hakuri akan abindanai maka idress wlh nasan naci maka mutunci amma dan allah kataymakeni kayafemin wlh alhakinka yamakani narasa yadda zanyi dan allah kayafemin idrees kaji dan allah. Idan da ace agabana takemin maganan zan iya rantsewa hawayene afiskarta lokacin datake wannan kalaman, nai shiru kamar bazance komaiba daga baya kuma saina tuna ...

NASHA WAHALAR SOYAYYA kashi na 4

NASHA WAHALAR SOYAYYA CONTINUETION .............:...................: CIGABA---- CIGABA----- CIGABA. HAJARA nazuwa saita watsamin wannan ruwan natsaneka idi, bana kaunarka, maikaunarkama banasonsa, kai bama kaiba hatta danginku da yan uwanku bana sansu matsiyaci mai zuciyar kare, Tana gama kalaman tajuya tawuce gida bata saurari abinda zanyi mata raddiba natsaya wata zazzafar kwalla ke fitowa tacikin idanuwana tana kwararowa zuwa kan kumatuna daga karshe tamike kan hakar karin wuyana, bantaba tsammanin wannan wulakanci daga hajaraba bama wannan wulakancinne kawai bacin raina tsananin munanan kalaman dataymin shi sukafi gundurata tundanake bantaba jin haushin hajaraba daidai dana mint daya sai awannan lokacin naji natsaneta naimata tsanar da ko shaidan baimatashiba tabbas dole yau zan rabu da hajara koda kuwa ita kadaice macen aduniya, nadan shanshani ruwan datazubamin ruwan sabulune yayi kama dana wanki kokuma na wanke wankene oho. Nadan taka kadan zan tapi nakara tsayawa, nadan karata...

nasha wahalar soyayya kashi na 3

,,........:........: CIGABA........CIGABA....... Ban bari rabi takarasa maganar datakeson fadaba na katseta tokuma saime naga duk wasikunki haba rabi mai kikeso nace miki? Ina kikeson nasaka kainane? Yakamata kibarni da abinda yake damuna. Rabi tace Allah ya huci zuciyarka tunda naga yau kana fishi bari nabari sai gobe ko sauraronta banyiba naji karshen kalamanta nadora tapiata nai gaba. Karfe daya da rabi aka taso su hajara kafin sannan kuwa tuni nakasance akan wannan mugun itacen wanda namaidashi kujra ta ta dole. Aikuwa ina zaune ina waige waige kamar wani marar gsky kawai sainaganta tabayyana ma ana sun dawo daga makarantar dam!!! Gabana yafadi amma dayake nayi nisa sainacigaba dayi matamayataccen kallona wanda bana kosawa dayiwa hajara irinsa aikuwa karaf sai idona yahade danata, wata mummunar harara ta harbomin saikace wadda tahada ido da mutuwarta dasauri namaida kaloona kasa kasa gabana na dukan uku uku a ah waime yasa hajara take hakane ninamarasa mai yasa yanxu nake tsoranta ...

NASHA WAHALAR SOYAYYA, -kashi 1

NASHA WAHALAR SOYAYYA, ------------------------------ CIKAKKEN LABARIN,,,,,,, Yauma kamar kullum nazauna akan bushashshen itace dayake kallon gidansu hajara, idona tsuru akan kofar gidan sonake kawai tafito naganta naji dadi, tsawon minti talatin inajira amma fa shiru wai maye yaci shirwa, cikina ya dameni da kugi na yunwa sai alokacin natinama ashema kokaryawa banyiba wata hamma nadanyi sannan na tashi tsaye daga kan bushashshen itacen yayin danaga wani yaro yafito daga gidansu hajaran dakayan makaranta ajikinsa. Tabbs nagane yaron shine wanda suke tapia makaranta da hajara kullum take rike masa hannu amma abin mamaki yau kuma shi kadai yafito. Kai to amma ina hajara kardai ace kobata da lpy? Kokumadai wani abune yasameta, nan take naji nakasa samun sukuni nai sauri nasha gaban yaron,,,,,,,, sulaiman yau kiuma ina yayar taka yayi dan murmushi sbd yaron akwai fara a sosai yace tab aitatapi mkrnt yau tace bazata tsimayeniba dan sunada wani assignment kuma dawuri za a hada, shiyasa, damm...

NASHA WAHALAR SOYAYYA 2

NASHA WAHALAR SOYAYYA CONTINUETION ----2 :::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::::: AKOFAR GIDANSU rabi at nafaka kamar hadin baki ina tsayawa wata yarinya tapito daga gidan dasauri nai kiranta nace tashiga gidan takiramin rabi aikuwa bata dadeba tapito akace wanene nace tace idrees ne takoma nanma bata dadeba tapito tace tanazuwa wannan karon ban bawa yar aiken komaiba sbd bakomai a aljihun sai godiya dana ambata mata tawuce zama nagyara sosai danbansan me rabi zataceminba intapito nidai nasan zai wahala ta iya yafemin wulakanci danai mata amma abinda nake dayakini rabi mai ilimice dan haka innai mata wata nasihar watakil ta iya yafemin abinda nai mata, salamun alaikum!! Karaf muryar rabi naji akunnena nan take takatsemin tunanina nai saurin juyowa sainaga tajuyamin bayanta, gaba dam!! Azuciyata nace lallai shikenan yau rabi zata rama wulakancin danai mata, karfin halinai nasha gabanta wata nustsuwace tazomin koda muka hada ido da ita sai tay sauri ta sunkuyar dakai. Nafar...

SUNAYEN WASU MAZA DA HALAYEN SU ...

SUNAYEN WASU MAZA DA HALAYEN SU ... 1- ABBA: son mata, ji da kai, surutu, kuma mostly yan gata ne ga kokari da addini 2- GARBA Kazanta mako, most of them basu waye ba 3- SADEEQ @ zuciya, taurin kai, ga son musu 4- ADAMU Yawancin su duk gajeru ne, ga katon kai, son gardama, ga kwadayi 5- UMAR/FARUQ zuciya, suna da kirar gardawa wa sun su 6- AHMED shiru shiru ga zurfin ciki 7- ALIYU zuciya ga iya tsara mace 8- IBRAHIM akwai addini, da kwakwalwa, yawancinsu bakake ne, ga iya tsara mace 9- JAMILU son gayu, son gulma kamar mace 10- SALIHU shiru shiru, abun tausayi hmmm 11- AMINU basa magana, amma akwai iyayi da tsari 12- SHAMSUDDEEN sun iya bayar da labari, gasu da karya 13- AUWAL yiwa mata karya, son burga da kudi 14- SAIFULLAHEE Karyar kudi, bagu da fafa 15- FAYSAL da ZUBAIRU kuna jin sunan, ba sai na fada ba, sai dai Akwai masu basira da kwakwalwa 16- ABDULLAHI hakuri, kawaici, rashin son abun duniya 17- DADDY / HALIFA shaye shaye, bin mata, da maula 18- ANAS wawaye ne most of them, doga...

lbr masoyiya. ta

Masoyiyata, abar qaunata, kuma sirrin rayuwata ta kasance sau da yawa takan qirqiro qarya domin ta kare kanta a duk lokacin da muka samu sabani a tsakaninmu, tsabar son da take yi min da gudun kada ta bata min rai ne yasa take yin hakan. Yau da gobe yasa a hankali na gano hakan, sai nayi tunanin me yakamata nayi ne? Shin in qyale ta ta cigaba tunda tana yine don ta faranta mini kokuwa? A qarshe na yankeshawarar in hana ta yin qarya, duk abinda ya faru ta fada min gaskiya kawai, indai zata yi qarya akan ta faranta min to kuwa lallai abinda yasa tayi laifin tun farko yafi qarfinta ne, sannan irin son da nake yimata da kuma yarda da ita da nayi na tabbata in tana da dama ba zata taba saba min ba. Tun daga lokacin dana kwabeta akan qarya sai yazamo duk ma abinda ya faru sai ta gaya min gaskiya; nikuma sai inji na fahimtu sai inyi mata afuwa. Bazan iya misalta muku irin QARFIN DA SOYAYYARMU ta qara ba saboda fadawa juna gaskiya, lallai bahaushe yayi gaskiya da yake cewa Gaskiya Dokin Qarfe ...

kamar yah?

A lokacin kyakkyawan Matashin yake zaune shi kadai kamar maye a can qarshen ajin, ya tattara hankali da nutsuwarsa ga fuskar wayarsa, bai lura da wata farar tauraruwar budurwa sanye da zungureren hijabi wacce take tsaye a kansa ba. "Hafizu ina ta magana." Muryarta mai tafiya da hankali, a karo na farko ta baqunci kunnensa. Ya d'ago da kansa ya zuba mata ido. Qwaqwalwarsa ta shiga tariyar wani al'amari da ya faru gare shi a wani lokaci, lokacin da Hadiza tazo masa da baqin albishir wai ya d'irka mata ciki daga kawai taje suyi extra lesson kafin daga bisani ya aikata lahira. Yanayi da halin da yake ciki yanzu ya saje da wancan lokacin, sai dai wannan ba Hadiza ba ce, wannan ta zarce Hadiza komai ta fuskar cikar halitta, wannan farar tauraruwa ce mai haske, mai murmushin sace zuciya. Ta guri d'aya ta kwafsa, ta tashi ta zura wani uban Hijabi kamar matar Liman. Kyakkyawar budurwar ta jefe shi da murmushinta firgita samari. Ya ja gwauron numfashi tare da kawar da k...

IDAN KAINE ZAKA KOMA KUWA? __

IDAN KAINE ZAKA KOMA KUWA? _ ____________ _ ____________ _ wani saurayi yaje tadi gurin budurwarsa. Suna cikin fira kawai saiyaga saibudurwar tamiqe tayi tafiyarta gida batare da tace sai anjima ko sai gobeba. Kamar da wasa sama da minty goma bata dawoba. Kawai saiya hau mashin dinsa yatafi gida. Bayan yaje gida yashigar da mashin daki kenan kawai saiyaji wayarsa tana ring. yana dubawa sai yaga budurwar nan tashice ta kira. Koda yadaga wayar saiyaji tace "WAI KAI DAGASKE TAFIYA KAYI? LALLAI NAYARDA BAKA SONA SOSAI" yabude baki daniyar yabata amsa kawai saiyaji tace to yanzudai kadawo ina jiranka domin akwai maganar danakeso zamiyi dakai. Wai idan kaine budurwarka taimaka haka zaka koma kuwa_______________ _ ____________ _ wani saurayi yaje tadi gurin budurwarsa. Suna cikin fira kawai saiyaga saibudurwar tamiqe tayi tafiyarta gida batare da tace sai anjima ko sai gobeba. Kamar da wasa sama da minty goma bata dawoba. Kawai saiya hau mashin dinsa yatafi gida. Bayan yaje gida yas...

mafarkina 1

Ina zaune tazo ta rufemin ido ta baya,can sai ta cire hannunta ta ruga da gudu cikin daki,na mike na bita da gudu ina zuwa muka fara wasa irin na masoya,tana jifana da matashin kai/pillow,nima ina jifanta dashi... Can sai na tashi naje wajenta,tana zaune bisa gado na duka domin na rungumeta, dukawata keda wuya sai naji na kwalla ihu nace,"wayyo Allah mama"...nan da nan mommy na da dad dina suka shigo dakina da gudu domin suga meya faru,suna zuwa suka ganni kwance a kasa na kone a kirji, basu ko tsaya jin meyafaru ba suka sungumeni zuwa asibiti.. Ina asibiti abokina mai suna Lawai yaxo gaisheni,to shine Lawai yake tambayana wai ya akai na kone? nacemai wlh na daura ruwa a risho domin in dafa indomie(abinka da mare mata)sai nadan kashingida kafin ruwan yai zafi, to kwanciyata keda wuya sai nafara mafarkin muna soyayya da ASABABU to a mafarkin nawane naje rungumeta sai akai rashin sa'a na rungume risho shine na kone a kirji. * to gwauraye da tuzurai idan za ai bacci a rinka...

kataba ganin idon basira

KATSAYA KAYI DUBA DA IDON BASIRA 1.Ka zama mai tausayi. 2.Mai yawan tuba. 3.Mai bin Sunnah. 4.Mai taushin Zuciya. 5.Mai yawan kyauta. 6.Mai saukin kai. 7.Mai yawan Hakuri. 8.Mai yawan kyautatawa Mutane. 9.Mai Afuwa da rangwame. 10Mai kyautatawa Maraya. . 11.Mai tausayawa dabbobi. 12.Mai yawan karatun Qur'ani. 13.Mai yawan yin Nafilfili. 14.Mai Tausayawa yara. 15.Mai girmama na gaba 16.Mai biyayya ga iyaye. 17.Mai yawan Ambaton Allah. 18.Mai Tunawa da mutuwa. 19.Maikyautatawa Makoci. 20.Mai Girmama bako. 21.Mai sada zumunci. 22.Mai bawa Mutane Uzuri. 23.Mai raka gawa Maqabarta. 24.Mai Tausayin talakawa da nakasassu. 25.Mai kyakykyawar mu'amala da mutane. 26.Mai karban Gaskiya. 27.Mai zuwa Masallaci da wurin wa'azi. 28.Mai amfani da lokutan ka wurin aikata alkhairi. 29.Mai Farin ciki da cigaban musulunci. Dama sauran halaye na kwarai. 30.Kada ka zamo mai yin Bidi'a da Shirka. 31.Kada ka dinga bincika laifukan mutane. 32.Kada ka rinka yin gulman mutane. 33.Kada ka rinka yi...

waya

NETWORKS! Yadda zaka duba number dinka na mtn idan baka saniba=> *663# yadda zaka koma mtn ipulse *406# yadda zaka zaka sayi 5mb a 5 naira 406 2# sannan 406 1# yadda zakayi double rechg crd 885 pin card # shikenan yadda zaka duba kuma *886# yadda zaka sayi 82mb alayi zain amma namasu andriod ne 440 18# shikenan yadda zaka koma essyliq a layin etisalat 244 1# yadda zaka duba mb a etisala *228# yadda zaka duba mb a mtn *559# yadda zaka koma mtn zn *400#

wakan janaba

YADDA A KE WANKAN JANABA * *********************** da farko zaka fara kar kato botikin da yake gabanka bayan ka shiga da ruwa matsaftaci, Sai ka wanke hannunka sau uku, Sai ka wanke duk kan inda najasar ta shafa, San nan sai kayi tsarki, alokacin da zaka yi tsarki a lokacin zaka ɗaura niya a zuciyarka/ki. San nan sai ka ɗaura alwala kamar yadda kake yi a kowace sallah, ƙafa ce kawai baza ka wanke ba. San nan sai ka tsoma hannunka cikin ruwan sai ka murza a kanka ka tabbata ko ina ya samu har sau uku,(saboda a lokacin da janaba ta sameka kofofin gashin jikinka budewa sukeyi idan ka kwara ruwa akanka zai iya yi maka illa shiyasa akafiso ka tsoma hannunka ka murza a kanka dan kafofin gashin su rufe). San nan sai ka ɗebo ruwa ka dinga kwarawa ɓarin gefen jikinka na dama kana cuɗawa ko ina ya samu, sannan ka wanke gefen jikinka na hagu shima ka cuɗa ko ina ya samu. Idan kagama wanke jikinka duka da ruwa san nan sai ka wanke ƙafarka cikon wannan alwala da ka fara. Shi ke nan ka ko kin kammal...

dariya

Ba'a . Dariya. BUDURWA Saurayi: ladidi antashi lfy budurwa:Silent... Saurayi: ladidi ankusa daura mana aure amma harynzu baki daina mun wulaqanci ba budurwa: hmm chammaka dai saurayi: daman ba wani abune ya kawo ni ba illa in tambaye ki ko kin iya tuki. Domin ina son matata na ta kware a tuki budurwa: hmmm tanimu kenan shiyasa nake matukar sonka. Saurayi: ummn budurwa:to wace irin mota za ka siya mun saurayi: mota kuma!!! Budurwa: eh mana ba yanzu ka tambayen ko na iaya tuki ba. Saurayi:chap chap ni fa tukin tuwo nake nufi Buhun masara Aka bani. Hahaha

waseeqar soyayya 1

Waseeqar Soyayya 01 NEMAN AMINCEWAR SOYAYYAR KA ! Assalamu Alaikum Warahmatullah" bayan shinfidaddiyar sallama wacce addini na ya tanadar, ya harkokin yau da kullum ? Ya lafiyar ka ? Bayan haka, kada kayi mamakin ganin wannan waseeqa tawa ko kuma shedan ya yaudare ka cewa kada ka amince dani domin nayi tallar kaina a gare ka" sam kada ka yarda da hakan, yazo a hadisan manzon Allah (s.a.w) cewa a zamanin sa mataye suna zuwa ga maxaje suna neman amincewar su domin suyi Aure. Don haka neman SOYAYYAR namiji a wajen mace ba rashin aji bane ko zubar da qima, wannan shine cikakken aji da kyautatawa domin munyi koyi da bayin Allah na kwarai. Suna na xxx, wata kila ka sanni,wata kila kuma baka sanni ba. A wata rana ina tafiya na hadu da kai a hanya. Cikin ikon Allah sai naji na kamu da soyayyar ka sakamakon ganin kamalar ka,ilimi,hankali,iya ado,dss. Zuciya ta ta aminta da kai ta fara azabtar da gangan jiki na! Lallai ina bukatar agaji daga gare ka don haka zan so ka ziyarce ni ta han...

lecturer

Wani lecturer ne mai hannu 1 ya shiga lctr hall.. hausa yake koyarwa...shigarsa ke da wuya ya rubata sunan topic din da xaiyi magana akai.....KARIN MAGANA....bayanya koyar da su ma,anar sa da yadda yake da misalan sa..,sai yace an gane aka ce eh....sai yace to idan an fahimta waye xai bashi misali guda 1.... Can sai wata ta daga hannu..sai ya bata ixinin ta fada... Sai tace...misali hausawa na cewa"hannu daya 1baya daukar jinka"...sai yayi shiru xuwa wani lkc kana ya dubeta yace "eh hakane amma yana iya ba da carry over dan uban mutum"............

alamomun cikawada imani

ALAMOMIN CIKAWA DA IMANI MANZON ALLAH S.A.W YACE= 1. Wanda kalmarsa ta karshe ita ce LA'ILAHA'ILLALLAH 2. Da wanda ya mutu da gumin goshi. 3. Da wanda ya mutu ranar juma'a 4. Da wanda aka kasheshi a wajan jihadi. 5. Da wanda ya mutu agurin ya da addini. 6. Da wanda ya mutu saboda wata Annoba. 7. Da wanda ciwan ciki ya kasheshi 8. Da wanda ya mutu a cikin ruwa 9. Da wanda ya mutu ta hanyar gobara. 10. Da wanda gini ya ruso masa. 11. Da matar data mutu gurin nakuda. 12. Da wanda tarin fika(TB) ya ya kasheshi. 13. Da wanda ya mutu sakamakon ciwon 6arin jiki. 14. Da wanda ya mutu wajan kare dukiyarsa amma ta halak. 15. Da wanda ya mutu wajan kare mutuncin iyalinsa. 16. Da wanda ya mutu gurin kare rayuwarsa. 17. Da wanda ya mutu gurin kare rayuwar al'umar musulmi da dukiyarsu. 18. Da wanda ya mutu yana aikin alkairi, kamar sallah, hanyar zuwa ziyara, karatun Qur'ani, da sauransu. 19. Da wanda wani shugaba azzalumi ya kasheshi dan ya tsaya akan gaskiya, kuma yana gaya mas...

mal.buba

MALAM BUBA A SAUDIYYA..... Wani mutum ne mai suna malam buba yaje saudiyya aikin hajji...sai aka sauke shi a dakin laraban da basa jin hausa...gashi shi kuma bai iya larabci ba.... Sai bukata ta kamashi ya shiga toilet dan biyan bukatar sa ya rufe kofar toilet din...shigar sa ke da wuya sai wuta ta kama a cikin tailet din yayi kokarin bude kofa amma hakan yaki samuwa.....gashi yarasa ta yadda xai kira wadannan larabawan su fahimci abin da yake nufi su kawo masa dauki.......... Kawai sai ya fara kiran MALAM BUBA FIN_NAR....MALAM BUBA FIN_NAR...... Yaji shuru babu wani motsi...sai ya kara daga murya yace.."MALAM BUBA FIN_NARI KHALIDEENA FIIHA ABADAA"........., kunga laifin sa.......kuma wannan dan wanna gari ne haka........ni dai nace dan garin su oh oh ne?????

naija

Boko Haram Sun Kashe Mutane 45 A Jihar Borno Wasu 'yan bindiga da ake zargin 'yan kungiyar Boko Haram ne a jiya Litinin sun kai hari wani kauye da ake kira Dille da ke jihar Borno, inda suka kashe mutane sama da 45 tare da kona gidaje, wuraren ibadu da shaguna, wanda hakan ya sa jama'ar garin kauracewa gidajensu suka shiga daji domin tsirar da rayuwarsu. Bincike ya nuna cewa 'yan bindigan sun shigo kauyen ne da jerin gwanon motoci sama da ashirin yayin da wasu kuma ke kan babura. Kamar yadda wani mazaunin garin mai suna Njimtiku Papka, wanda ya bayyanawa manema labarai a Meduguri ta waya cewa 'yan bindiga sun yi ta harba bindiga ne kan mai uwa jawabi a yayin da duka shigo kauyen.

wasanni

WASANNI:Nijeriya Na Tsaka Mai Wuya Saboda Hukumar NFF Nijeriya na cikin hadarin kasa cika wa'adin da Fifa ta gindaya na ranar Talata domin maido da jami'an hukumar kwallon kasar - NFF wandanda ta cire. Gwamnatin Nijeriya na cikin rashin tabbas ne saboda yajin aikin da ma'aikatan shari'a ke yi. Maudu'o'i masu alaka da wasannin. A makon daya gabata ne Fifa ta dakatar da Nijeriya daga shiga harkokin kwallon kafa saboda zargin gwamnati na katsa landan a harkar kwallon kasar. Sai dai gwamnatin ta ce ta cire jami'an NFF ne bisa umurnin wata babbar kotu a jihar Filato. Idan har Nijeriya ba ta maidoda shugabannin NFF, a karkashin jagorancin Aminu Maigari ba, to kasar ba za ta halarcin gasar cin kofin duniya ta mata 'yan kasa da shekaru 20 da ake soma wa a watan Agusta a Canada.

allah subaha nahu wata ala yace

ALLAH (SWT) YACE: "HARAMUN NE KA SHIGAR WA IYAYEN KA, KO MUHARRAMANKA BA TARE DA YI MUSU SALLAMA BA" HATTA IYALANKA BA ZA KA SHIGA GARE SU BA SAI DA SALLAMA. (Q: NUR 59.) "Ya ku wadanda sukayi imani! Wadannan da hannuwanku na dama suka mallaka da wadanda basu isa mafarki ba daga cikin ku, su nemi izini sau uku, daga gabannin Sallar alfijir, da lokacin da kuke ajiye tufafin ku, saboda zafin rana, kuma daga bayan Sallar Isha'i. Su ne al'aurori uku a gare ku, babu laifi a kanku kuma babu a kansu a bayan su. Su masu kewaya ne a kanku, sashen ku akan sashe." (Surutun Nur, aya ta 58) A takaice ladubban shiga gida sune, dukkan yaron da ya balaga dane ko bawa, kada ya shiga gida ko dakin mahaifin sa ko uban gidan sa a a bayan sallama, har sai in an amsa da ya shigo, in ance ya koma, ya koma. In kuma yana zaton ko ba'a ji bane, to ya maimaita sau uku. Neman izini wajibi ne ga yayanka baligai a lokutan nan uku, kamar yadda yazo a aya ta 59, daga gabanin sallar Alf...

martabar mata a musulinci

MARTABOBIN MATA A TARIHIN MUSULUNCI MACE CE Take da darajar samun suna a cikin jerin sunayen Surorin Al-Qur'ani Me Girma. (Babu Sunan Sura Maza sai Mata Suratun NISA'I). MACE CE Ta fara yin sa'ayi tsakanin safa da marwa (HAJARA A.S). MACE CE Sanadiyyar Musuluntar Sayyidina Umar R.A (NANA FATIMA A.S) MACE CE Shari'a ta tanadar mata ladan jam'in salloli guda biyar da Jumu'ah Da Jana'iza Da Jahadi Duk ba sai ta je ba,amma sanadiyyar ta kyautatawa mijinta,Allah zai bata duk ladan wadannan ibadun. MACE CE Tayi Sanadiyyar Tsiran Sahabbai daga Fushin Allah lokacin da akayi sulhun Hudaibiyya MACE CE ta shawo kan sahabbai har suka tsira daga fushin Allah. (UMMU SALAMA R.A). MACE CE Ta kwantarwa da Manzon Allah (S.A.W) hankali lokacin da Ifk ya faru a Madina,kafin saukar wahayi. (BARIRA). MACE CE Ta Fara taimakawa Manzon Allah (S.A.W) kuma tana daga cikin Wadanda suka fara karbar Musulunci a duk duniya,kuma ta yiwa addini hidima da dukiyarta da duk abinda ta mallaka h...

izala

Kungiyar Izala Ta Yi Kira Ga Gwamnati Da A Kawo Karshen Cin Zarafin Da Ake Wa 'Yan Arewa Mazauna Kudancin Kasar Nan Kungiyar Izala ta kasa ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta kawo karshen cin zarafin yan Arewa da ake yi a Kudancin kasar nan. Kiran ya fito ne daga bakin shugaban kungiyar na kasa Ash-Sheikh Imam Abdullahi Bala Lau a lokacin da yake gabatar da tafsirin safiyar Litinin (17 Ramadan) a garin Jimeta da ke Jihar Adamawa. Shugaban ya ci gaba da cewa Gwamnatin Tarayya ta gaggauta kawo Karshen cin Zarafin 'yan yankin Arewa da akeyi a kudanci yayin neman abinci cin su. Shehin Malamin yayi kiran ne jim kadan bayan da sojoji suka yi farauta tare da awon gaba da yan arewa a Safiyar Litinin a garin Yanagoa dake jihar Bayelsa Wadanda basu jiba basu gani ba, duk da zuwa yammaci an sako dukkanin wadanda aka kama ba tare da an samu wani da laifi ba. Babu nutsuwa ga mutanen Arewa a yayin zamansu a kudancin la'akari da abin da ya faru a jihohin Abia, Imo da na baya bayan nan a...

gaisuwa

AMSA DA YARENKA {Gaisuwar bangirma a gareku} 1. Good morning - ga Turawa 2. Sabahul khair - ga Larabawa 3. Barka da asuba - ga Hausawa 4. Otutu oma - ga Inyamirai 5. Ekaaro - ga Yarbawa 6. Bonjour - ga Faransawa 7. Guten morgen - ga Jamusawa 8. Gu[]amôrni[]ga - ga Indiyawa. 9. Zaô an - ga Yan China 10. Ohayôgozaimasu - ga Yan Japan AMSA DA YARENKA KODA KUWA BA'A LISSAFO SHI ANAN BA... SO MUKE MU SAN YAREN DA YAFI YAWA A WANNAN SHAFIN NAMU. MUNA FATAR KUN WAYI GARI LAFIYA.

bil jannah

ASHARATUL MUBASHSHIRUNA BIL JANNAH. _ ___________ Manzon Allah (S.A.W.) yanada Sahabbai kemanin guda 120,4000. Amma akwai wasu kebabbu, zababbu, fitattu wadanda akayi musu bishara da gidan Aljanna tun sunada Rai a wannan duniya. Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) yafada a hadisi cewa: Anyi musu bishara da gidan Aljanna, wato sune: ASHARATUL MUBASHSHIRUN. Wadannan Sahabbai sune kamar haka:- (1) Abubakar Saddiq (R.T.A). (2) Umar Bin Khaddab (R.T.A). (3) Usman Bin Affan (R.T.A). (4) Aliyu Bin Abi Thalib (R.T.A). (5) Dhalha Ibn Ubaidullah (R.T.A). (6) Zubair Ibnul Awwam (R.T.A). (7) Abdurrahman Bin Auf (R.T.A). (8) Sa'ad Bin Waqqas (R.T.A). (9) Sa'id Bin Zaid Bin Amr (R.T.A). (10) Abu Ubaidah Bin Jarrah (R.T.A). Allah Madaukin Sarki yabamu albarkacin wadannan bayi nasa.

mutum

MUTUM NA IYA SAMUN RABONSA TA HANYAR HARAMUN....... Watarana Sayyadina Aliyu Ibn AbiDalib yaje wani gari sai ya tsaya kofar wani masallaci domin yin sallar walaha dan haka sai ya kira wani yaro ya bashi rikon dabbarsa rakumi ko doki ya shiga yana shiga sai yaronnan yaga cewa lalle wannan igayar da aka daure dabbar idan an kaita kasuwa za'a samu kudi mai dan kauri dan haka sai kawai ya kwance igiyar ya gudu kasuwa da ita koda Sayyadina Aliyu ya fito yaga haka sai samu wani bawan Allah kuma yace masa akwai yaro mai kama kaza kaza ka bishi ka sayomin igiyar dabbar dake hannunsa ka dawo ni kuma na baka riba mutumin yabi yaro ya kuma same shi ya taya igiya darhami daya shi kuma ya sallama masa ba wata gardama yana zuwa yayima sayyadina Aliyu bayanin yadda sukayi sai kawai Sayyadina Aliyu yace Allahu Akbar kaga ya ci rabonsa ta hanyar haramun domin kuwa dama nayi niyyar da ace ya tsaya na gama na fito to zan bashi kyautar dirhami guda to amma gashi yanzu ya samu dirhamin amma kuma ta han...

sunusi II

Sabon Sarkin Kano Mai martaba Alh- Sunusi Lamido Sunusi, Yayi Zama Da "Yan Majali Sunsa, Wato Fadawan sa kenan, A'inda Yake Tambayar su Cewa: Shin Kowan Nenku Yayi Aikin Hajji Kuwa?. Sai Suka Amsa Masa Dacewa Ranka Shidade Acikinmu Babu Wanda Yatabayin Aikin Hajji. Maimar Taba Anan Take Yace Dasu: Kuje Kuwaro Mutane Sitti 60 Daga Cikinku Anbiya Musu Umara, Guda Talatin Kuma Anbiya Musu Aikin Hajji... Sannan Kuma Arananne Yasanya Dokan Cire Takalmi Wai Don Anshiga Cikin Fadar Kano, Saidai Za'acire ne Awajenda Shari'a Tace Acire, Kama Tundaga Tabarmar Da Akeyin Sallah Akanta,Damaka Mancinta. Sannan Sabon Sarki Maimar Taba Sunusi Lamedo Sunusi, Yayi Qarin Albashiwa "Yanmajali Sunsa Kamar Haka. Wanda Yake Daukan Naira Dubu Goma 10,000, Yakoma Naira Dubu 30,000. Medaukan Naira Dubu Ishirin 20,000 Kuma, Yakoma Naira Dubu 60,000. Wannan Shine Dalilinda DaYasa Nace,Mutuwan Wani Tashin Wani. Allah Yakara Mana Irin Wadannan Shuwa Gabanni Awannan Kasa Tamuta Najera Amin.

dariya dole

DARIYA DOLE: sunan labarin kenan: wani mai kifine wanda yake soyawa abakin titi yana sayarwa, wata rana yafito dakayansa saiya soya kifinsa yagama gaba daya cansai hadari yataso saiya kwashe kayan yashigar dasu shago shigarwarsa kedawuya sai hadarin yawuce sai yadebo kayan yadawo dasu. Sai hadarin yakuma dawowa, saiyakuma kwashe kayan yakai shago sai hadarin yakuma wucewa saiya kuma dawo dakayan kifin, dawowarsa keda wuya sai hadari yakuma dawowa saida akai haka sau'uku anahudun saiyace wallahi bazai kwasheba sairuwa yasakko kamar dabakin kwarya kawai saiya koma shago yazauna yazubawa kifin ido ruwa yana tadukan kifin, can sai aka dauke ruwa saimai kifi yafito yazo wajen teburdin kifin kawai saiya taba kifin yaga duk yalalace babu wanda zai moru duk yaratattake , can saiya daga kansa sama saiya sauke yakuma kallon kifin, kawai saiyace kuma mutum yayi magana ace ZA'A SASHI AWUTA. Hahahahahaha:

wata rana

Wata rana akayi musu tsakanin dan sarkin baccin kano da dan sarkin baccin Adamawa. Dan sarkin baccin kano ya kwanta bakin wata fadama bacci ya daukeshi har ruwan damuna yazo ya gangara dashi cikin rafin nan kifi ya hadiyeshi shikuma kifin kada ta hadiyeshi ita kuma kadar dorinar ruwa ta hadiyeshi sai watarana mafarauta suka kama dorinar suka yanka suka fede suka dauko kada acikin cikinta suka fede kadan sai sukaga kifi acikin cikinta suka fede kifin saiga mutum a ciki duk wannan abun da akeyi bai farka ba saida aka tashe shi sannan ya farka yana farkawa sai ya hau fada yana cewa daga fara baccina sai atasheni? Sai shikuma dan sarkin baccin Adamawa. Shikuwa dan sarkin baccin Adamawa ya kwantane a gindin wata bishiya sai ruwan damina yazo ya gangara dashi cikin kogi sai wata rana gabar kogin ta zabtaro ta fada masa a kai daganan sai wata bishiyar kuka ta tsiro akansa kuka ta girma harta tsufa sai wata rana iska mai karfi tazo ta kada bishiyar, mutane suka taru suna kallon kukar sai suka ...

dan gal

DUK WANDA BAYA DANGALE WANDO, DOMIN BA MAMAKI YIN HAKAN YA KAISHI WUTA!!! saboda hadisan ma'aiki (saw) da dama da sukayi gargadi akan jan tufafi da barinsa ya wuce idan sawu. daya daga cikin hadisan shine: ﻗﺎﻝ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ " ﺃﺯﺭﺓ ﺍﻟﻤﺴﻠﻢ ﺇﻟﻰ ﻧﺼﻒ ﺍﻟﺴﺎﻕ ﻭﻻﺣﺮﺝ ﺃﻭ ﻻ ﺟﻨﺎﺡ ﻓﻴﻤﺎ ﺑﻴﻨﻪ ﻭﺑﻴﻦ ﺍﻟﻜﻌﺒﻴﻦ ﻣﺎ ﻛﺎﻥ ﺃﺳﻔﻞ ﻣﻦ ﺍﻟﻜﻌﺒﻴﻦ ﻓﻬﻮ ﻓﻲ ﺍﻟﻨﺎﺭ ﻣﻦ ﺟﺮ ﺇﺯﺍﺭﻩ ﺑﻄﺮﺍ ﻟﻢ ﻳﻨﻈﺮ ﺍﻟﻠﻪ ﺇﻟﻴﻪ « daga abu sa'idul khudri (r.a) yace Manzon Allah (saw) yace: KWARJALLEN MUSULMI RABIN QWABRI NE, BABU LAIFI YAKAI TSAKANIN QWABRI DA IDON SAWU. ABINDA YA WUCE IDON SAWU, AWUTA YAKE. WANDA YAJA KWARJALLENSA DON TAQAMA ALLAH BAZAI DUBESHI BA imam abu dauda ya ruwaitoshi acikin sunan nasa hadisi na 4093 DAN HAKA DUK WANDA YAKE BARI KAYANSA NA JAN KASA, YA TABBATAR BADA MA'AIKI YAKE KOYI BA,KUMA YASABA KARANTARWAR MANZON ALLAH (SAW)

nasiha

WANNAN NASIHANE DA WANI YAYIWA DANSA KAFIN YA MUTU (1) Na dandani jindadi amma banji abinda yafi lafiya dadiba (2) na dandani daci da bakinciki amma banji abinda yafi bashi nauyiba. (3) nayi dakon karfe amma banji abinda yafi bashi nauyiba. (4) naga wadata dayawa amma banga abinda yafi watatar zuciyaba. (5) nayi hakuri kuma na dandani wahala amma banga abinda yafi talauci wahalaba. (6) naga makiya dayawa amma banga makiyinda yafi shaidan ba. (7) na sanya tufafi dayawa amma bansanya kamar tufafin tsoron Allah ba. YA ALLAH MUNA MASU ROKONKA CIKIN KANKANCIN BANGASKIYARMU KAYI MANA JINKAI. KA GAFARTA MANA KURA-KURANMU ALLAH YASA MUCIKA DA IMANI

ABUBUWAN DA SUKE RUSHE MA MUTUM LADAN AZUMINSA:

ABUBUWAN DA SUKE RUSHE MA MUTUM LADAN AZUMINSA:  Malamai sunce akwai wasu ayyukan Zunubi wadanda duk da cewa basu karya Azumi, amma suna rushe ladansa. Wadannan abubuwan sun hada da: 1. QARYA: Qirkirar labarai na Qarya domin ayi dariya, ko kuma domin wata manufa wacce bata inganta ba. 2. QAULUZ ZOUR da kuma aiki dashi : Maganganu marassa tushe yayin da aka dangantasu da wani wanda bai ji ba, bai gani ba. 3. QAZAFI: shima wani nau'I ne na Qarya da ake yi domin 'bata sunan Mutane. 4. GULMA : Shi ma wani nau'I ne na Qarya da Qauluz Zour. 5. ANNAMIMANCI: daukar magana daga wajen wani, ka kaita wajen wani da niyyar 'bata tsakaninsu, ko kuma don neman shiga awajen wani. 6. RANTSUWAR QARYA : ita ma nau'I ne na Qarya da Qauluz Zour. Yazo acikin hadisin Bukhary: "Duk wanda bai bar Qauluz Zour da kuma aiki dashi ba, to babu ruwan Allah don yabar cin Abincinsa da shan abin shansa

mai kudi

Wani mai kudine, yana da 'yan aiki guda biyu da wata 'yar wanke-wanke, dakuma mai gadin gida , Watarna sai matarsa tapita xuwa asibiti, yaran su kuma suna makaranta saiya aiki maigadi xuwa super market , saiya kira 'yar wanke-wanke yanemeta itama ta amsa yashiga daki da ita suna kwance , saiga yaronshi daya ya dawo daga makaranta Yana zuwa sai kawai yatura kofa yana shiga daki saiya taradda babanshi da 'yar wanke-wanken gidansu Sai baban yayi sauri yatashi ya kirawoshi xuwa waje yace "ga dari biyar 500 dinnan kada kapadawa kowa", sai yaron ya fashe da kuka yace: "Wlh kudin yayi kadan Jiyama da naxo na tarar da mama tare da mai gadi kaman yadda kuke yanxu haka tabani dubu 5 tace kada nagayawa kowa , amma kai dari biyar xaka ban, wlh sai ka karamin" In kaine Ya xakai ?

jarumta

KU DUBA WANNAN JARUMTAR:- Watarana Anje YAQIN UHUD Sai Ake Cewa Sahabbai An Kashe ANNABI(S.A.W) Sai Wata Mai Suna 'UMMU KALLABI' Ta Ji Labarin Sai Ta Zare Takobinta Ta Hau Kan Ingarman Dokinta Ta Zo Filin Yakin:- Tana Cewa:"Ina ANNABI (S.A.W)?? ?" Sai Aka Ce Mata:"KUTILA ABUUKI" Wato An Kashe Babanki, Sai Ta Ce:"LAN AS'ALAKA ABI ABIN" Wato Ban Tambayeku Baba Na Ba Sai Suka Sake Cewa Ai Bayan Babanki Ma:"Zaujiki Fulamun Kat Kutila" Sai Ta Ce:"Ban Tambayeku Miji Naba" Ina Tambayarka Ina ANNABI (S.A.W)?? ? Sai Suka Sake Ce Mata:"ABUKI FULAMIN KATKUTILA" Sai Ta Ce:"LAN AS'ALUKA ABI ABIN WA AN ZAUJI WA AN AKHI WALAKIN AS'ALAKA AN RASULULLAH" Sai Suka Ce Mata:"In Zaki Iya Kije Can Ga ANNABI(S.A.W) An Kewaye Shi An Sassare Shi". A Hakan UMMU-KALLABI Ta Tafi Kafin Ta Isa Wurin Da ANNABI (S.A.W) Yake Sai Da Aka Yi Mata Sara Da Suka Sau 12 a Jikinta, Da Zuwanta Wurin Da ANNABI (S.A.W) Yake Sai Ta ...

A wata ruga

A wani rugar fulani ne an hadu za'ayi meeting da daddare, sai aka rarrabawa mata kyadir da ashana kowacce ta kunna a kan teburin da mijinta zay zauna. Aka ba wa matar Sarkin Ruga ma nata domin ta kunna a teburin mijinta kafin ya iso. Daga zuwan sa sai ya ga hasken kyandir akan kowanne tebur amma banda nasa. Nan da nan ya fara masifa, Sarkin Ruga: in banda iskanshi yaya za a she teburin kowa da haske amma banda nawa? Masu rabo: A'a ranka ya dade mun ba matarka kyandir da ashana ta kunna a teburinka. Sarkin Ruga: ke ina kyandir din da ashana da aka baki? Mata: A'a an bani ashana amma ban ga a-shi-balbal din ba. Masu rabo: Ba a-ci-balbal ba, wannan farin abun mai zare da muka baki. Mata: Oho...aradu ina she ROGO ne, she na shinye!

s. a. w

Wata rana Annabi ya wuce ta wani waje sai yaga ana ganawa Bilal azaba, ran Annabi bai yi dadi ba. Ya samu Sayyadina Abubakar yace masa, Ya Abubakar lallai ana azabtar da Bilal saboda Allah. Sakamakon kaifin hankali irin na Abubakar sai ya fahimci abin da Annabi yake nufi, kai tsaye ya je gida ya kwashi kudi makudai ya tafi wajen Umayyata bin Khalaf yace masa, shin zaka sayar min da Bilal? Yace kwarai kuwa mai zanyi da wannan wulakantaccen bawan. Ya tsugawa Abubakar kudi, amma Abubakar ko ragi bai nema ba ya zaro kudi ya bashi, la’asar na yi Abubakar ya je wajen Ka’aba ya bada sanarwar cewa ya sayi Bilal kuma ya ‘yantashi saboda Allah. Shi yasa duk lokacin da aka ce Abubakar shugabanmu, to sai Umar ya kara da cewa “KUMA WANDA YA ‘YANTA SHUGABANMU BILAL”… Allahu Akbar, Allah ya kara yarda da kai Ameen.

Jami'an Tsaro Sun Gano Wasu Makamai Da Aka Binne A Dajin Balmo

Jami'an Tsaro Sun Gano Wasu Makamai Da Aka Binne A Dajin Balmo Jami'an tsaro na kasa sun gano karin makamai da aka binne a cikin Dajin Balmo, wanda ya tashi daga Jihar Bauchi ya dangana da Jihar Jigawa. An kuma ce ya makwabci Dajin Sambisa wanda ke Jihar Borno inda 'yan kungiyar Boko Haram ke da sansanoni. Wata sanarwa da kakakin hedkwatar tsaron, Manjo Janar Chris Olukolade, ya fitar, ta ce sojoji suna tonon wadansu wurare ne a dajin da nufin gano makaman da aka binne lokacin da suka yi kicibis da manyan bindigogi goma, da bindigogi masu sarrafa kansu fiye da 80, da kuma jigidar harsasai da dama. Sanarwa ta kuma kara da cewa an kuma gano makaman harba rokoki da sauran kayan yaki masu yawa. Janar Olukolade ya kuma ce sojoji sun gano kayan jami'an tsaro ciki har da rigar kariya daga harbin bindiga

Sayyiduna Salmanul Farisy (ra) ya ruwaito cewa Manzon Allah (saww) yace:

: Sayyiduna Salmanul Farisy (ra) ya ruwaito cewa Manzon Allah (saww) yace: "DUK WANDA YA CIYAR DA MAI AZUMI KUMA YA SHAYAR DASHI DAGA ABINCI DA ABINSHA NA HALAL, TO MALA'IKU ZASU YI MASA ADDU'A ADUK SA'O'IN (MINTUNA, AWOYI) DA SUKE CIKIN RAMADHAN, KUMA MALA'IKA JIBREELU (AS) ZAI YI MASA ADDU'A ADAREN LAILATUL QADRI". (IMAM TABRANI ne ya fitar da hadisin acikin Alkabeer)

alheri danko

ALHERI DANKO NE BAYA FADUWA KASA BANZA.. Wani mutum ne ya hau mota irin hayis dinnan zashi wani waje sai da yazo sauka saiya duba domin ya biya kudin motar sai kuwa yaga babu kudin da yake aljihun sa. ya duba ya duba amma yaga babu kudinnan,nan da nan kwandastan motar ya fara surutu yana zage zage wai dama irin halin wasu mutanen kenan sai su hau mota basu da kudi suce wai kudin sun fadi. mutuminnan yayi rantsuwa da Allah akan kudinnan faduwa sukayi, amma kwandasta da direba suka ki yarda suka ce ai sai ya biya ko kuma suyi masa dukan tsiya. mutuminnan har ya fara hawaye saboda takaicin sunce masa barawo ne shi kwandastan ya sauko daga motar ya shake masa wuyan riga zai fara yi masa duka. sai wata mata acikin motar tace su dakata,ta dauko kudin motar mutumin ta biya masa sannan ne kwandastan ya kyale shi. mutumin ya dubi matar nan zai mata godiya,sai tace masa''karka damu kaima ka kyautata wa wanda kaga yana neman taimako''a haka suka ja motar suka tafi bayan kwana biyu...

istigfari

Istigfari (neman gafara) da tuba zuwa ga allah. Manzon allah tsira da amincin allah sutabbata a gareshi, yace Na rantse da allah! Ina neman gafarar allah kuma ina tuba zuwa gareshi, A kowace rana sama da sau saba'in- kuma yace, yace tsira da amincin allah su tabbata A gareshi: 'yaku mutane! Ku tuba. zuwa ga allah Domin ni ina tuba a kowace rana zuwa gareshi sau dari. kuma yace, tsira. Da amincin allah su tabbata agreshi : wanda yacce:ina neman gafara allah wanda babu abin bautawa dagaskiya sai shi , rayayye mai tsayiwa da komai kuma ina tuba zuwa gareshi Allah zaigafata masa zuunbansa koda zuubin gudu daga fagen fama ne . kuma. Yace tsira da amincin allah su tabbata a gareshi mafi kusanci da allah yake kasancewa da bawansa a tsakiyar.karshen dare ne. Don haka idan kana da ikon kasancewa cikin masu abaton allah a wannan lokac,toka kasance. kuma. Yace tsira da amincin allah su tabbata a gareshi mafi kusanci da bawa yake kasancewa daubangijinsa yayin da yake sujada nedon haka ku y...

annabi sulaiimn

TARIHIN ANNABI SULAIMAN(A.S).. BIRNIN DA ANNABI SULAIMAN(A.S)YAKE TAFIYA DA SHI ACIKIN ISKA. Annabi sulaiman(A.S)yana da birni(gari)wanda yake tafiya a kansa an ginashi da 'kwarir girmansa kamu DUBU GOMA(10,000)acikinsa akwai tarago guda biyu, acikin kowane tarago akwai duk abinda miskinai suke bu'kata,tarago na 'kasa yafi 'karfe kauri da 'karfi karago na sama kuma yafi ruwa garai-garai da sirantaka, wanda yake cikinsa yana ganina abinda yake wajen taragon saboda garai-garai d'insa, acikinsa akwai wata 'kubba fara, akansa akwai wata tuta fara wacce take haskakawa askarawansa haske idan dare yayi. KUJERAR ANNABI SULAIMAN(A.S) Allah Ubangiji(S.W.T)yana cewa:- "MUNJEFA JIKI KAN GADONSA, "suratun sad aya ta 33.  An ruwaito cewa Annabi sulaiman(A.S)ya umarci shaid'anu da suyi masa kujera wacce zai ringa zama akai don yin hukunci wato Al'kalanci, ya umarcesu da suyi mata 'kira wacce idan wani mai 'Barna ko wani mai shaidar zur ...

Azumi

FATAWOYIN AZUMIN RAMADAN. Tamtaba ta 64: MENE NE HUKUNCIN YIN AZUMIN SHIDA A CIKIN WATAN SHAWWAL (WANDA AKA FI SANI DA SITTU SHAWWAL)? Amsa: Yin azumin sittu-shawwal sunnah ce wadda Manzon Allah (Sallallahu Alaihi wasallam) ya yi, kuma Sahabbansa suka yi. Haka kuma, magabata na kwarai sunyi. Hadisi ya tabbata daga Abu Ayyub al-Ansari (Radhiyallahu Anhu) ya ce: Manzon Allah (Sallallahu Alaihi wasallam) ya ce: "Wanda yayi azumin watan Ramadan, sannan kuma ya bishi da azumi shida a cikin watan Shawwal, to kamar ya yi azumin shekara daya ne 102." Sai dai ajwai wadanda suke ganin karhancin wannan azumin, kuma suna jingina wannan magana zuwa ga Imam Malik. Amma shi Imam Malik bai yi inkarin wannan Hadisin ba. Sai dai ya yi inkari ga wanda ba zai iya bambancewa tsakanin azumin Ramadan da Sittu-Shawwal ba. Watau don gudun kada ya hada su a jere da tunanin duk wajibi ne shi ya sa Imam Malik ya kara da cewa: Labari bai zo mini cewa magabatan Madinah suna yin wannan azumi ba. Domin tsor...