Ramadan khareeeem
BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM. Allah kayi salati da aminci abisa zababben zababbu, Annabinmu Manzonmu kuma Shugabanmu Muhammadu, tare da iyalan gidansa Inuwar al'ummah, da Sahabbansa Jagororin gaskiya. Yau insha Allahu zamu Qarasa magana akan Falalar Azumi sannan muci gaba da bayani akan rabe-raben Azumin da kuma falalar watan Ramadhan. 4. Hadisi daga Sayyiduna Abu-Umamah Albahily (ra) yace: "Nazo wajen Manzon Allah (saww) nace masa: "Ka Umurceni da wani abinda zan aikata wanda zai shigar dani Aljannah". Sai yace min "NA HOREKA DA YIN AZUMI. DOMIN HAKIKA BASHI DA MAKAMANCI". Sai na sake dawowa wajensa karo na biyu (Na sake tambayarsa akan haka). Sai yace min "NA HOREKA DA YIN AZUMI". (Imamu Ahmad da Hakim da Nisa'iy ne suka ruwaitoshi). 5. Daga Sayyiduna Sahlu bn Sa'ad Assa'idy (ra) daga Manzon Allah (saww) yana cewa: "HAKIKA ALJANNAH TANA DA WATA QOFA WACCE AKE KIRA "RAYYAAN". IDAN RANAR ALQIYAMA TAYI, ZA'A CE "IN...