brazil
Dan wasan Brazil Dani Albes ya ce ficewar kasar Spain a gasar cin kofin duniya tun a zagayen farko babban darasi ne ga kasashen da ke fafatawa a gasar. A cewar dan wasan na Barcelona samun nasara ba karamin kalubale ba ne. Spain ce ta lashe kofin duniya a kasar Afrika ta Kudu a 2010 kuma a bana tun a tashin farko ne aka yi waje da Spain bayan ta sha kashi a hannun Holland da Chile a rukuninsu na B. “Wannan abin kunya ne”, a cewar Albes tare da yin jaje ga abokan wasan shi na Spain a Barcelona. Wannan dai kamar kira ne Albes ya ke yi wa ‘Yan wasan Brazil don su dage musamman yadda Medico ta rike su babu ci kafin su hadu da Kamaru a ranar Litinin domin samun hurumin tsallakewa zuwa zagaye na gaba.
Comments
Post a Comment