Posts

Showing posts from December, 2014

MB DATA TRANSFER

ZAka iya yin transfer na MB da layinka na MTN TO MTN kawai kabi wadannan matakan na kasa, amma ka tabbata kana da MB mai yawa kamar 10MB. 1. Zaka yi rijistar transfer din tura MB, domin yin rijistar danna 131 2*1# zasu turo maka da sako kamar haka, "Y'ello, you have successfully registered your MTN Services, your default pin is 0000." 2. Bayan ka samu PIN naka 0000 saika canza shi, domin canza PIN naka "texting 'CHANGE OLDPIN NEWPIN NEWPIN' to 131." ko kuma ka danna 131 2*2# saikai reply da tsohon PIN wato 0000 zasu ce kasa sabon har sau biyu wato wanda kake so. 3. Idan kuma baka da MB akan layinka kuma kana son saya, saika danna 131 2*3# ko kuma 123 4# saika zabi na yadda kake son saya. 4. Sannan kuma sai wanda zaka turawa, MB akan layinsa. Wato "Share Data to beneficiary" kafin ka turawa mutum MB ka tabbata yana cikin "beneficiary" naka, domin sa lamba a beneficiary" saika danna 131 2*4*1# saikai reply dan lambar wanda kake so ...

takai

Zan Maida Kano Yadda Take Lokacin Shekarau Idan Na Zama Gwamna - Takai Malam Salihu Sagir Takai, dan takarar gwamnan jihar Kano, a karkashin jam'iyyar PDP, ya ce idan yayi nasarar zama gwamna zai yi kokarin ganin maida jihar kamar yadda take a lokacin mulkin tsohon gwamna Malam Ibrahim Shekarau. ...Ko Kanawa na son Kano ta koma yadda take a baya, a lokacin mulkin Malam Shekarau, Sardaunan Kano?

FA'IDA GA MATA MASU SON GASHINSU YAYI KYAU KUMA YAYI TSAWO.

Image
FA'IDA GA MATA MASU SON GASHINSU YAYI KYAU KUMA YAYI TSAWO. Kamar dai Yadda muka sani kuma kuma kara tunatarwa cewa karin Gashi kowanne irine haramun ne kuma Annabi (saww) ya tsoratar da mu game da Karin kowane irin gashi, sannan kuma ya tsinewa duk maccen da take karin gashi da wadda ke karawa mutane din. In shaa Allahu ga hanya wadda zaki samu gashin kai ba tare da ke shiga sahun wadanda tsinuwa zata fadawa ba kuma in shaa Allahu ko kan ki kwalkwal yake kika bi wannan hanya zaki dace da Iznin Allah. A nemi garin Hulba kamar cokali 4 haka a dafa shi a cikin Ruwa, ya dahu sosai, sannan a sauke idan ya huce, sai a shafa wannan garin da kuma ruwan a kai. A cakuda shi sosai da gashi, zuwa kamar Mintuna 15 ko 29 sai a wanke kan da sabulun Habbatus-sauda, ko ta Zaitun. Bayan an yi wannan, sai a nemo wadannan mayukkan; Man Darbegijya, Zaiti-lauz, Man Zaitun, Man Ridi, Man Kwakwa, Man Alayyadi, Man Habbatussauda. Idan aka same su, sai a hada su waje daya, a zuba su a wani waje rika shafaw...

ALLAHU AKBAR!! Ya Zo a Tarihi Cewa:-

ALLAHU AKBAR!! Ya Zo a Tarihi Cewa:- Wata Rana Annabi MUSA(A.S) Ya Tambayi ALLAH Madaukakin Sarki Cewa:- "Ya UBANGIJI! Ta Yaya Zamu Gane Cewa Kana Fushi Da Mu???" "Kuma Ta Yaya Za Mu Gane Cewa Muna Cikin RahamarKa???" Sai ALLAH Madaukakin Sarki Ya Ce Da Shi:- "A Duk Lokacin Da Kuka Ga Na Daura Muku Shuwagabanni Wadanda Baku Jin Dadinsu, To Tabbas Wannan Lokacin Kuna Cikin Fushi Na, Sannan a Duk Lokacin Da Kuka Ga Na Daura Muku Shugabanni Kuna Musu Fatan Alkhairi, Suna Sonku Kuna Son Su, To Tabbas Kuna Cikin Rahama Ta". ALLAHU AKBAR! KAMAR YANDA: SAYYIDIL-WARA(S.A.W) Ya Ce:- "Kamar Yadda Kuke To Haka Za'a 'Dora Muku Shugabanni" SANNAN: ALLAH Ta'ala Yana Cewa:- "Lalle ALLAH Ta'ala Ba Zai Canjawa Al'umma Halin Da Suke Ciki Ba, Har Sai Sun Canja Da Kansu" DON HAKA MU FARA KUKA DA KANMU AKAN MATSALARMU.... ALLAH Ya Ba Mu Ikon Gyarawa Ya Kuma Yasa Muyi Taubatan Nasuha Wacce Zai 'Karba, ALLAH Yasa Mu San Kanmu Da Kanmu,...

YADDA ZAKAI EDIT THEMES NA WAYA NOKIA DA KANKA. . .

YADDA ZAKAI EDIT THEMES NA WAYA NOKIA DA KANKA. . . ta hanyar amfani da blueftp idan bakadashi shiganan kai download http://haqqfiles.t15.org/load/file/27/BlueFTP.html DA FARKO GA ABUBUWAN DA AKE BUKATA DAN HADA THEME = BLUEFTP = FOLDER = THEME = HOTUNA >Blueftp dashi ake hada theme din. >Empty folda kuma itace folder din da babu komai acikinta. >Sai kuma shi Theme yazama kana da wani theme din awayarka. >Sai kuma Hotuna wato wanda zakasa amatsayin naka. GA YADDA AKE HADASHI Kahau kan Blueftp dinka ma'ana kabudeshi, idan budewarka ta farko ce zai nunoma tutoci dayawa sai kazabi ta farko wato ta Birtaniya ma'ana kazabi turanci kenan.. Daga nan zai ta tambayarka 'allowapp to access' sai kana dannan YES wato bangaren Hannun hagun... Idan yagama zai nunoma kan Waya da kuma kan memorynka wato alamar C: / da kuma E: /, Sai kazabi inda theme dinka yake wato wanda zaka hada wani dashi kenan, Idan kajekan theme din sai kadanna OK na wayarka, Anan ma zai tambayeka sai...

Wata Sabuwa! Matan Nijeriya Ne Mafi Iya Yaudara A Duniya

Wata Sabuwa! Matan Nijeriya Ne Mafi Iya Yaudara A Duniya Sakamakon wani binciken musamman da aka gudanar, an gano cewa matan kasar Nijeriya su ne a layin farko na matan da ke cin amanar maza a doron duniya. An samo wannan rahoton ne daga wani gidan talbijin a kasar Indiya mai suna, INDIAN TbNEWS, inda ya nuna cewa matan da suka fi yin fice a bangaren cin amanar aure, gami da yaudarar maza su ne wadanda suka fito daga wadansu kasashe guda takwas, inda Nijeriya ta kasance ta farko a rukunin. Mashahurin kamfanin nan mai sarrafa koron-roba, wato ‘Condom,’ DURED LTD. ne ya gudanar da binciken. Inda ya bayyana cewa, kafin hada alkaluman, sai da suka tattaunawa da kimamin mutane dubu ashirin da tara a kasashe daban-daban har 36 na duniya, sannan uka bi kadin al’amuran da ke faruwa a cikin kasashen, bayan nan ne aka bayyana sakamako. Ga yadda alkaluman binciken nasu ya tabbatar: Nijeriya: Kashi 62 cikin 100 na matan Nijeriya suna yaudarar mazajensu. Thailan: Ita ce kasa ta biyu, inda binciken ...

HUKUNCIN KARBAR KYAUTAR IDIN KIRSIMETI DA CIN ABINCIN WANNAN RANA KAMAR YADDA SALAFUS SAA'LIH SUKA YI BAYANI

HUKUNCIN KARBAR KYAUTAR IDIN KIRSIMETI DA CIN ABINCIN WANNAN RANA KAMAR YADDA SALAFUS SAA'LIH SUKA YI BAYANI 1- Da yake Alhamis mai zuwa ne Kiristoci za su fara abin da suke kira bukin kirsimeti (idin kirsimeti) wanda suke yin shi ko dai a ranar 25/12 M ko kuwa a ranar 7/1 M. 2- Sannan da yake a Nigeria ana zaman cakuda ne tsakanin su Kiristoci da kuma al'ummar Musulmi. 3- Sannan da yake shi Musulunci addini ne da ya bayyanar da hukuncin dukkan wani lamari da ya shafi rayuwar dan Adam, ko dai ta hanyar nassi, ko ta hanyar zahiri, ko ta hanyar ishaarah da iimaai. 4- Sannan da yake akwai masu bidi'ah da dama da ke halatta abin da Shari'ah ba ta halatta ba, ko haramta abin da Shari'ah ba ta haramta ba, lalle ya dace a yi wa al'ummar Musulmi bayanin hukuncin abin da ya shafi wannan Idi na Kirsimeti ta bangarorinsa da ke iya shafar wasu al'ummar Musulmi. * *********************** To amma kafin mu shiga bayanin wadannan hukunce-hukunce ya kamata Musulmi su san abu...

KASASHEN WAJE: Skype Ya Kirkiro Tsarin Fassara Harsuna

Image
KASASHEN WAJE: Skype Ya Kirkiro Tsarin Fassara Harsuna Kamfanin Microsoft ya kirkiro tsarin fassara hirar da masu amfani da Skype ke yi a harshen Ingilishi da Spaniyanci. Wadda hakan zai faru ne yayin hira ko tattaunawa ta bidiyo a Skype, masu magana da wadannan harsuna za su iya fahimtar junansu. Wannan na nufin an samu ci gaba wajen fassara harsuna a tsarin Skype. Gurdeep Pall na kamfanin Microsoft ya ce an samu wannan nasara ne sakamakon bincike na sama da shekaru 10.

SHIN JONATHAN ZAI YI YAWON KAMFEN KUWA A AREWA MASO GABASHIN KASAR MU KUWA?

Image
SHIN JONATHAN ZAI YI YAWON KAMFEN KUWA A AREWA MASO GABASHIN KASAR MU KUWA? A Najeriya, yayin da manyan jam'iyyun kasar biyu suka fitar da 'yan takarar shugabancin kasasu, wani abu da za a mayar da hankali a kai shi ne zuwa yakin neman zabe. Jam'iyyar PDP mai mulkin kasar dai ta sake tsayar da shugaba Goodluck Jonathan domin ya fafata da Janar Muhammadu Buhari, wanda jam'iyyar adawa ta APC ta tsayar. Hukumar zaben kasar dai, INEC ta amince 'yan takara su yi yakin neman zabe daga yanzu har zuwa farkon watan Fabrairu, lokacin da za a fara kada kuri'a. Wata tambaya da 'yan kasar ke yi ita ce: shin shugaba Jonathan zai je yakin neman zabe a yankin arewa maso gabashin kasar da ke fama da hare-haren 'yan Boko Haram? Jonathan bai je yi wa mazauna yankin jaje ba Dalilan wannan tambaya na da dama, amma babba daga cikinsu shi ne: • Tunda 'yan Boko Haram suka karfafa kai hare-hare musamman a wannan shekarar, shugaban bai kai ziyarar jaje yanki ba. Wannan mataki...

WANI AIKI SAI BUDURWA

Image
WANI AIKI SAI BUDURWA 1. Ka saya mata waya ta kira wani da ita. Kai kuma tama please call me 2. Kai mata kyauta ta bawa wani saurayin . Idan ka tanbaya tace baka yarda da ita bane 3. Kaje wajenta zance akan lokaci ta bata ma lokaci. Tace ma aiki takeyi 4. Ka damu da ita bakin ciki ya kashe ka. Karabu da ita kashiga damuwa 5. Kai mata dinki ta yiwa wani ado dasu. Idan kayi magana tace sunyi daddti 6. Kaje wajenta fira ka tarar da wani idan ka tambayi akasi a cema zama da saurayi daya matsala ne. 7. Ka dinga zance ta agun abokai, ita kuma ta dinga zagin ka gun kawayenta. 8. Ka ce yaushe zan dawo fira tace sai jibi, saboda wani saurayin zai zo. 9. Tasaka kuka kuma taki rarrashin ka. 10. Idan aka tambayeta a gidan su sai tace kai alhalin ba haka bane. 11, Ka kira wayarta kaji buzy ka tambayeta tace wata anty nace na kirani, 12, Ka nuna kishinka a kanta, tace ma ka fiya takura mata, Ohhhh mu maza ina zamusa kanmu....??? Amma fa ni tawa duk bataimin hakan....

wayyo ALLAH

Image
*Mama Mai Yasa Kike Kuka? *Mama Kidaina Mun Kuka?? *wayyo mama kidaina kuka? >Ni Ina Cikin Neman ALLAH >Nida Bana Zina >Nida Bana Karya >Nida Bana Cin Amana >Nida Ba'a Bina Bashi >Nida Nake Zikirin ALLAH Koda Yaushe >Nida Nake Karatun Al'Qur'ani Kuma Ina Aiki Dashi >Nida Bana Zalunci >Nida Bana Wasa Da SALLAH >Nida Bani Da Abokan Banza >Nida Bana Gulma Da Mutane >Nida Bana Raina IYAYENA >Nida Bana Tare Da Mugayen Shuwagabanni >Nida Na Yarda Da Kaddara Mai Kyau Da Mara Kyau >Nida Na Ware Lokaci Dan Ganin Talakawa >Nida Nake Azumin Watan Ramadan >Nida Naka Zakka >Nida Nake Ziyaran Asibiti Na Taimakama Marasa Hali..! *Mama Kidaina Mun Kuka? Kice Suzo Suyi Saurin Kaine Makwancina Duniyan Nan Tana Mun Zafi........! *Babu Mai Jin Maganan Wanda Ya Mutu Sai ALLAH Madaukakin Sarki..! YAA ALLAH KASA MU FADI IRIN WADANNAN KALMOMIN NAN RANA DAKA DAUKI RANMU..!

:, MUSHAKATA

:, MUSHAKATA ,,,wani mutum ne yasayi sabuwar mota jeep shikenan kullum idan ya dawo daga aiki sai ya ajiye a wani kango da masu gadi yanabiyansu kudin gadi,to matsalar da yake fuskanta shine kullum da safe idan yazo sai yaga motar babu mai a ciki bayan kuma ya tabbata a cike ya ajiyeta, to abin yana damun sa domin masu gadi kullum sai suyi ta rantse rantse kan cewa basu bane ke satar masa mai ba , shikenan rannan sai yace sai ya kama wanda ke masa wannan abu bayan yazo yayi parking kamar kullum sai ya koma kujerar baya ya kwanta yayi lamo ,can tsakar dare sai kawai yaji ankunna mota anata sheka gudu akan titi amm fa bai ga kowa ba acikin motar ba can sai yaji kwadasta yana kiran pasinja yana cewa Istanbul,ne Ko Alkahira, ko Afghaistan hajiya indiya zaki je ne ko isra,ela, shikuma drir sai xuba wuta yake can sai yaji antsaya an dauki passinja anci gaba da tafiya can sai yaji driver ya juyo yacewa da kwandastan motar gaskiya yau motar nan akwai mai da yawa saboda haka zamuyi lodiin pasin...

ABUBUWA 91 DA ANNABI (SAW) YA NEMI TSARI DASU.

ABUBUWA 91 DA ANNABI (SAW) YA NEMI TSARI DASU. WADANNAN ABUBUWA DA SUKAZO A HADISAI ANNABI (S.A.W) YA NEMI TSARI DA SU. 1, ZUCIYAR DA BATA TSORAN ALLAH. 2, FITINAR ZUCIYA 3, SHARRIN, JI ,DA GANI 4, TSORO 5, ROWA 6, BAKIN CIKI 7, DAMUWA 8, BACIN RAI 9, HASARA 10, SABON ALLAH 11, KASALA 12, GAJIYAWA 13, KASKANCI 14, QARANCI 15, TALAUCI, 16, FITINAR KABARI, 17, ZUCIYAR DA BATA KOSHI. 18, YUNWA 19, CIN AMANA 20, TABEWA 21, MUNAFINCI 22, BASHI 23, FITINAR WADATA 24, FITINAR DUNIYA 25, SHARRIN MAZAKUTA 26, KAFURCI 27, BATA 28, RINJAYEN MAKIYA 29, DARIYAR MAQIYA 30, MUMMMUNAN TSUFA 31, MUMMUNAR HUKUNCI 32, TABEWA A RAYUWA 33, CIWON HAUKA 34, KAMBUN BAKA 35, QASQANCIN RAYUWA 36, KOMAWA BAYA A RAYUWA. 37, ADDU'AR WANDA AKA ZALUNTA. 38, MUMMMUNAR MAKOMA. 39, MUMMUNAN MAQOCI 40, RINJAYAN MAZAJE 41, FITINAR DUJAL 42, AZABAR JAHANNAMA 43, SHARRIN SHEDANUN MUTANE 44, FITINAR RAYUWA 45, FITINAR MUTUWA 46, AZABAR KABARI, 47, SHARRIN ABINDA AKA SANA ANTA. 48, SHARRIN ABINDA AKA AIKATA 49 , SHARRIN ...

GWAMNA DANKWAMBO YASHA DA KYAR A GARIN KASHERE.

ben.png GWAMNA DANKWAMBO YASHA DA KYAR A GARIN KASHERE. YANZU HAKA GARIN KASHERE DAKE KARAMAR HUKUMAR AKKO BA SHIGA BA FITA . Yanzu haka Al-ummar garin kashere sun farfasa motocin gwamnan jihar Gombe Alh. Ibrahim Hassan Dankwambo da tawagarsa a lokacin da ya shiga cikin garin kashere. Rahotanni na cewa a Ya zuwa yanzu dai an boye gwamnan a gidan sarkin kashere matasa kuma na cigaba da jifan gidan sarkin inda akayiwa jami'an soji waya saboda akwantar da tarzomar. Dama gwamnan na Gombe yana daya daga cikin gwamnoni 'yan gaba dai gaba dai din Jonathan ya zarce a 2015

AN TAMBAYI MANZON ALLAH (S.A.W).menene hankali ..

AN TAMBAYI MANZON ALLAH (S.A.W).menene hankali .. sai yace. 1 juriya akan bakin ciki 2.yin raha ga makiyi 3.barin mummunan zato 4.cire girman kai 5.karbar uzuri. 6.hakuri a inda kake da karfin ramawa .ALLAH KA BAMU IKON AIWATAR DASU. AMEEN

ALAMOMIN DAUKEWAR JININ HAILA

ALAMOMIN DAUKEWAR JININ HAILA Idan jinin Haila ya dauke akwai alama da shara'a ta sanya domin yazama shine manuniya akan cewar al'adarki ta dauke. Wadannan alamu sun kasu gida biyu kuma kowacce tana cin gashin kantane, sune kamar haka: 1. Bushewar Farji: Abinda ake nufi anan shine mace ta shigar da kyalle ko auduga cikin gabanta ta fito da ita busasshiya bawani jini a tare da ita, to da zarar taga haka to ta tabbata al'adarta ta dauke. 2. Farin Kumfa: wannan wani ruwane fari mai laushi da yake zuwa karshan al'ada, idan mace ta ga irin haka a karshan al'adarta to ta sani ta kammala. Wadannan alamomi sune suke nuna daukewar al'adar mace, idan mace bata taba ganin al'adaba sai a wannan karon sai tafara ganin bushewar gaba to kai-tsaye ta samu tsarki basai ta jira farar kumfaba. Amma idan wacce ta saba ganice sai taga bushewar gaba to malamai sukace zata dan saurara kadan domin jiran farin kumfa, amma jinkirin bazai kai ga fitar zababban lokacin sallah ba. A dun...

MIYA ME DANKALIN TURAWA

MIYA ME DANKALIN TURAWA => Dankali Nama Tumatur Albasa Attaruhu Kayan qamshi Gishiri Karas koren tattasai peas Maggi Butter ko mangyarda. => kisamu dankalinki mekyau kiferayeshi kidansa gishiri kadan saiki sa atukunya kidafashi, idan kina da bukata kina iya dakashi bayan yadahu kamar dai yadda xaki sakwara. Saiki samu kwarya/koko kishafa mai ajiki sannan kidinga mulmulawa kinasawa aleda. Idan kuma bakya bukata saki amfanidashi ahaka idanma manyane kiraba su biyu yadda xaixama madaidaita. Kinriga kinjajjaga kayan miyanki saiki daura mai awuta kisoya kayan miyan,sannan kixuba ruwa daidai misali kirufe kibarshi yatafaso sau daya. Dama kinriga kinsa maggi,gishiri kayan kamshi dadai sauransu. Saiki dauko dankalinki dayafara dahuwa daxu kisaka aciki, kikuma dauko peraren karas dinki kisanya saiki watsa peas dinki kirufe kibari su dahu. Idan suka dahu saiki dauko koren tattasan daga karshe kiyayyanka kixuba aciki, minti biyar yayi yawa xakiji wani rantsatsen qamshi natashi alamu yakamma...

YAM CAKE

YAM CAKE doya nama sugar maggi gishiri rabin cokali, curry, thyme kayan miya. Dafarko xakisamu doyarki mai kyau guda daya. Kifereta kiyanka daidai misali kizuba sugar babban cokali daya aciki saiki daura a wuta. Sannan kiwanke naman kisa thyme kiyanka albasa da maggi guda daya kisa ruwan daidai yadda xaidafa naman harya tsotse saiki kidaura bisa wuta har yadahu. Idan yadahu saki nikashi kokuma kidakashi da attaruhu kamar biyu tattasai daya kigoga albasa kixuba akan naman bayan kindaka kinsa maggi kijuya yahadu kisoyashi kamar danbun nama amma sama sama kamar minti goma, saiki yanka dafaffen kwai kamar guda uku ko hudu akai. Sannan kikoma kan doyarki data dahu kika sauke harma tafara shan iska, kimurmusheta ko kidaka sama sama kadadai tadaku sosai saimu xuba maggi da gishiri kisamu prayn pan wanda baya kamu, kixuba mai kamar cokali biyu ko uku. Sannan kiraba dakakkiyar doyar xuwa gida hudu namanma kiraba xuwa gida uku.saiki dauko doyar kashi daya kixuba acikin kaskon kidauki naman kashi...

LEMON ABARBA

Image
LEMON ABARBA Abarba Sugar. Flavour kisamu abarbarki mekyau daidai bukata, kiwanke ta tas kafin ki fere saboda xamuyi amfani da bawon, saiki samu faranti mekyau kibare aciki, idan kika gama ferewa saiki dauki bawon kisanya atukunya kisa ruwa daidai yadda xaki bukata kidaura awuta kibarshi yadahu. Saiki dawo wurin abarbarki ki nikata a blander kikawo ruwan bawon dakika dafa kixuba aciki kitace kisanya sugar da flavour kisa a fridge kokisa kankara. Idan yayi sanyi xakiji yadda xaibada ma'ana. Timeline Photos · Oct

%%CREAM CHICKEN SOUP%%

%%CREAM CHICKEN SOUP%% *kaza *madara *corn flour *gishiri da maggi *kayan qamshi. Dafarko xaki dafa kaza da dan kayan miya da kayan qamshi kisanya maggi da gishiri. Ruwan dan daidai xakisa yadda kobai tsotseba yaxamana kadan ne wanda yahau kai. Kixauna kixare kasusuwan yaxamana xallan naman kawai kika aje agefe guda. Saiki dama corn flour din kixuba akai hakama madarar damata xaki tare da corn flour din. Kimaida wannan tsokar kan wuta saiki xuba hadin madarar akai hadida juyawa ahankali saikirufe xuwa minti biyar saiki duba kiga idan kinaso dakaurine to idan bakauri saiki sanya ruwan xafi kijuya haryayi daidai da bukatarki..

O Allah Ya jikan IBRO ga kadan daga cikin FINA-FINANSA

Image
O Allah Ya jikan IBRO ga kadan daga cikin FINA-FINANSA 01. Ibro Baqin Mulki 02. Ibro Mulkin Mallaka 03. Ibro Karangiya 04. Ibro Awoilo 05. Ibro Jega 06. Ibro Mai Gyaran Waya 07. Ibro Mai Dalili 08. Ibro Wuta Sallau 09. Ibro Allo 10. Ibro Police 11. Ibro mai dawa 12. Ibro Dan Mallan 13. Ibro Bodigat 14. Ibro mai gidan biredi 15. Ibro Maja 16. Ibro Mazaje 17. Ibro Dan gatan Ibro 18. Ibro Yan,ya Mage 19. Ibro Kukere 20. Ibro Mai Kudi Uban Matsiyata 21. IbroHajiya Baba 22. Ibro Asibitin Kauye 23. Ibro Oga Abuja 24. Ibro Baban Direba 25. Ibro kwandasta 26. Ibro Mai Baba riga 27. Ibro Mai Ross 28. Ibro Suwaga 29. Ibro Kansila 30. Ibro Dan Sankarau 31. Ibro Da'u 32. Ibro Makaho 33. Ibro Dan jagaliya 34. Ibro Dan Garin nan 35. Ibro Dan Kasuwa 36. Ibro dan Almajiri 37. Ibro mai Kiran 38. Ibro Andimali 39. Ibro Amalala 40. Ibro Dorin Ibro 41. Ibro Dawa dai 42. Ibro Gabar Ibro 43. Ibro Akasa a tsare 44. Ibro Yar mai ganye 45. Ibro Bita zai-zai 46. Ibro alkali 47. Ibro Aloko 48. Ibro Angon Haj...

DAKUWA KAYAN DA ZA KI TANADA

Image
DAKUWA KAYAN DA ZA KI TANADA 1. Aya 2. Jar dawa 3. Masoro 4. Citta 5. Barkono 6. Kanunfari 7. Sikari 8. Kuli-kuli ko gyada 9. Man gyada YADDA ZA KI HADA Dakuwa tana daya daga cikin kayan gara da ake kai wa amare a kauye, ko kuma idan an yi haihuwa. A birni ma ana kaiwa lokacin da ake yiwa amarya gara, amma a zamanin da ne wannan yanzu an daina. Sai dai kawai ka ga ana yin ta domin sayarwa. Manya da yara duk suna cin dakuwa. Yadda ake yin dakuwa kala biyu ne, da wadda ake yi da jar dawa(kaura) da kuma wadda ake yi da aya. Za mu kawo muku yadda ake yin duka biyun. DAKUWAR DA AKE YI DA AYA Ki sami aya ki wanke ki rege idan da akwai tsakuwa kenan, sannan ki shanya ta ta bushe, sai ki soya ta, idan tayi sai ki kai inji a barza. Idan an dawo da ita sai ki zuba a turmi ki fara dakawa, ki kawo gyada ko kuli-kuli ki zuba, amma gyadar ba a soya ta da gishiri, ki zuba kayan kanshi wato barkono da citta da masoro da dan gishiri dan kadan ki cigaba da dakawa. Haka za ki yi ta dakawa har sai kin ga ...

KAYAN DA ZA KI TANADA DON YIN NAKIYA

KAYAN DA ZA KI TANADA DON YIN NAKIYA 1. Shinkafar tuwo 2. Sikari 3. Kanunfari 4. Citta 5. Masoro 6. Barkono 7. Man gyada YADDA ZA KI HADA Ki sami shinkafar tuwo ki wanke ki shanyata ta bushe, idan ta bushe sai ki zuba a kwarya ki zuba citta da kanunfari da masoro da dan barkono ki kai inji a niko ko kuma idan kina da karfi ki zage ki daka da kan ki har sai tayi gari, ta dakan idan an yi nakiyar tafi gardi, sai dai dakan ne da wuya. Don haka gara ki kai inji a niko miki, idan an niko sai ki saka rariya mai laushi ki tankade sai ki soya garin sama-sama, idan kin gama sai ki shanya ta a tabarma domin ya huce kuma ya dan sha. Sai ki kawo sikarinki ki dafa shi, idan ya dahu sai ki bari ya huce sannan ki zuba shi a cikin wannan garin shinkafar ki ringa juyawa da muciya har sai kin ga ya hade, ki kawo man gyada dan kadan ki zuba ki tuka sosai, sannan sai ki zuba a cikin turmi a kirba har sai kin ga ta kirbu kuma nakiyar ta fara sheki, sai ki kwashe ki cura.

•Duk abinda kakeyi daure ka karanta wannan darasin rayuwar•

•Duk abinda kakeyi daure ka karanta wannan darasin rayuwar• Wata rana wani malami yana so ya karantar da dalibansa wani darasi, sai ya sami takardar naira dubu daya (₦1000) sabuwa fil, sai ya shiga ajinsu, dama daliban yawansu ya kusan kai dari biyu...... Shigarsa ajin ke da wuya sai ya daga dubu dayan yace wanene me son wannan? Sai kowa ya daga hannu, tunda malamin yaga haka sai ya yamutsa dubu dayan duk ta kudundune. sai ya sake cewa to waye kuma me so??? Sai kowa dai ya sake daga hannu..... Sai malamin ya aje kudin a kasa yasa takalminsa ya tattake ta duk tayi dumu-dumu da datti, sai ya dauka ya daga sama yace to yanzu kuma waye me so??? Ai kafin ma ya rufe baki yaga hannuwa dai sun cika aji ma'ana kowa yana so kenan....... Sai malamin yace yauwa to ku dakata dalibai dama wani darasi nake son ku koya....yanzu ku duba duk yadda nayiwa kudin nan bai sa sonta ya fita daga zuciyarku ba, duk wannan kudundunewar da dattin dake jikin kudin bai rage darajarsa da komai ba —• To haka wani...

WACCE ZA KA AURA A CIKI?

WACCE ZA KA AURA A CIKI? Al’anaanah: Mace mai jinini da tsirtiya a kodayaushe, wadda kullum a shirye take ta kai karar miji ko saurayi, sannan ba ta da sirri ko na sisin kwabo. Al-manaanah: Mai yawan shimfida hannuwanta wajen bayar da kyauta ko alheri, amma idan abu ya faru a gaba, sai ta yi wa mijinta gorin cewa ta yi kaza da kaza domin shi. Al-hannanah: Mace mai tuna baya kan tsohon mijinta ko saurayinta, har ta rika cewa ai da wane ne, da ba zai yi mata haka ba. Ko kuma ta rika sambatu da sunan wani alhali tana tare da kai Al-Kannaanaa: Mace mai yawan surutu tare da alfahari da dukiyar iyayenta ko ‘yan’uwanta, musamman sarautar mahaifinta da sauransu. Al-hadaakah: Mai zuba idanu kan abin duniya. Komai ta gani sai ta nuna maita da kwadayinta a fili, ba ta iya boye abin take so, sannan za ta iya takurawa ta matsa lamba, ba za ta kwantar da hankalinta ba, har sai an saya mata, ta kowane hali. Al-barrakah: Mai yawan bata lokacinta wajen gyaran fuska domin birge maza, kuma ba ta damu da ...

Wazaki Aura A Cikin Mazan Arewa

Wa Za Ki Aura A Cikin Mazan Arewa? MAZAN ABUJA: Gayu da rainin hankali. MAZAN ADAMAWA: Karya, kalen dangi, jaraba. MAZAN BAUCHI: Rashin iya magana, Saurin Aure. MAZAN BINUWAI: Asiri, Bautar da mata da Son Kai. MAZAN BORNO: Alfahari da addini, kaya masu tsada da turare. MAZAN FILATO: Yaudara sai son wanka duk da talauci. MAZAN GOMBE: Zumunci, sai dai akwai jiji da kai. MAZAN JIGAWA: Kishin mata, kwalliya, matsin tattalin arziki. MAZAN KADUNA: Son harka da shiga sabgogin duniya. MAZAN KANO: Arziki amma akwai auri-saki. MAZAN KWARA: Ra’ayin Rikau, Son girma MAZAN KEBBI: Rashin iya zance, son gargajiya. MAZAN KATSINA: Salon soyayya, amanar aure, ashar ba a dauke ta a bakin komai ba. MAZAN NASARAWA: Zaman lafiya, Kabilanci, da ra’ayin rikau. MAZAN NEJA: Rike aure, gidadanci. MAZAN SOKOTO: Wariya, yawan kula mata, rashin wayewa. MAZAN TARABA: Daraja aure, amma ba tsafta. MAZAN YOBE: Hakuri sai dai akwai asirce mata. MAZAN ZAMFARA: Son na banza, yi wa mata hidima.

save your money

YADDA ZAKA RUFE KUDINKI A CIKIN WAYA Nasan kusan kowa yasan wannan amma duk da haka wadansu na tambaya ta akan in kara yin bayani akan yadda ake kulle kudin kira a cikin waya . follow bellow steps 1.kawai danna wannan code din 33 0000# domin rufe kudinka: idan kayi haka baka da damar da zakayi kira har sai ka cireshi. 2.idan zaka cire sai ka danna #33*0000# domin bude kudinka

TARIHIN IBRO A TAKAICE

Image
  An haifi marigayi Rabilu Musa Ibro a shekarar 1971. Ya yi karatun Firamare dinsa a Danlasan da ke cikin karamar hukumar Warawa. Sannan kuma ya yi Sakandare a Kwalejin horon malamai ta Wudil (Teachers College). Daga nan ne ya shiga aikin gidan Yari (Prison Service) a shekarar 1991. Ya yi shekara takwas Ya na aikin Gandiroba inda ya kai matakin insfekto, daga nan ne ya bari ya cigaba da sana’ar wasan kwaikwayo. Rabilu Musa Ibro ya fara sana’ar Fim a tun ya na aji uku na makarantar sakandare. Ya na da Mata da Yara hudu ko uku akwai : Jamila, Kubra, Auta. Daga cikin yaransa akwai: Akwai Faisal, Jawahid, Lawiza, Abdul-Mummuni, Sannan akwai Asma’u, Annabe, Sa’adiyya, Akwai wani yaro kuma da ya Haifa ya sa sunan mai gidansa wato Baba Yaro. Kafin Rasuwarsa Ya bayyana Ciroki a matsayin dan wasan hausa abokin sana’ar sa da ya fi burgeshi. Da aka tambayi Rabilu Musa ibro dan wasan santimental da ya fi burgeshi sai yace “ Adamu Usher, ka ga wannan, yana bani sha’awa. Saboda ba shi da girman kai,...

Nima sunana Halima ko A gida

Wani mutum ne yake yi wa matarsa kuri wai shi jarumi ne. Rannan tafiya ta kama su, ya yi shirin yaki. Suna tafiya cikin wani daji sai ga dan fashi. Ya yi masu tsawa, suka tsaya cik. Da ya zo, sai ya tambayi matar sunanta, ta ce, Halima. dan fashin ya ce: “Kin yi sa’a, ban taba Halima, sunan mahaifiyata ne.” Ya juya wurin mijin, ya ce: “Kai yaya sunanka?” Sai ya ce: “Wallahi, ni ma ko gida Halima ake kira na kuma ka tambayi matata.”

’yan sholisho

Wasu ’yan sholisho ne suna cikin shan abinsu, sai daya ya dubi dayan ya ce: “Anya za mu shiga aljanna kuwa?” Sai dayan ya ce: “Yau ai abin taget ne. Tun da ga jama’a nan da yawa sun cika, kawai da ka faki ido sai ka rufta, kawai ka yi fuska!”

Nuna Nayi

Wani Babarbare ne aka kai shi asibitin mahaukata don a duba lafiyarsa. Da suka je sai ya hau wata bishiyar mangoro tun da safe har yamma bai sauko ba. Can sai ga shi diff a kasa. Likiticin suka ce masa: “Lafiya ka fado kasa?” Shi kuwa ya ce: “Nuna na yi, shi ya sa na fado.

Kwadayi Mabudin wahala

Wani Babarbare ne da Bafulatani suka fita yawo wajen gari, sai arnan daji suka kama su, suka kai su wajen sarkinsu. Shi kuwa sarkin sai ya nuna masu wani lambu ya ce su shiga su tsinki duk dan itacen da suke so. Bayan wani lokaci sai ga Bafulatani ya fito da manya-manyan mangwarori guda biyu a hannunsa. Nan take sarkin ya ce wa fadawansa su danne shi su saka masa mangwarorin a duburarsa. Nan take suka cika umurni, Bafulatani ya ci bakar wuya. Ya daga kai ke nan sai ya hango Babarbare, ya kuwa kece da dariya. Da aka duba domin a ga abin da yake wa dariya, sai aka ga ashe Babarbare ne ya tsinko manya-manyan kabewa guda biyu a hannunsa yana tahowa wajen sarki.

Hannu daya

Wani malamin jami’a ne mai hannu daya, yana cikin koyar da dalibai sai ya ce su kawo masa misalin karin maganar Hausa. Wani dalibi ya daga hannu ya ce: “Hannu daya ba ya daukar jinka.” Nan da nan sai malamin shi kuma ya ce: “Ba ya daukar jinka amma yana ba da carry ober (yana iya kada dalibi a jarabawa).

Dan Fulani Da Lemon kwalba

Wani Bafulatani ne ya kai ziyara birni wajen dan uwansa sai aka kawo masa lemon kwalba. Yana cikin sha sai ya ji gyatsa ta taso masa sai ya ce: “Rike mun nan, zan yi habo.” Bayan ya huta, sai ya ce wa dan uwansa: “Aradu Ja’e, wannan abin ya ji tsamiya da yawa!”

Direba da dan sanda

Wani dan sanda ne ya tsare direba, ga yadda tattaunawarsu ta kasance: dan sanda: “Ina takardun motarka?” Direba: “Ga su nan.” dan sanda: “Ina lasisinka?” Direba: “Ga shi nan.” (Komai aka tambayi direba yana da shi, dan sanda ya  gaza kama shi da laifi). dan sanda: “To wa ya ce ka rika tafiya kai daya a mota, idan wani abu ya same ka wa zai maida ka gida?” Direba: “Manzon Allah (SAW) ya ba mu wata addu’a, a duk lokacin da zan yi tafiya, idan na karanta ta, mala’iku dubu suna tare da ni.” dan sanda: “Mala’iku dubu a karamar mota? To ka yi obalodi, mu tafi ofis, na kama ka!

Madara ko omo?

Wani Bahadeje ne da ya je ci-rani birni, ya bukaci ya sha shayi sai ya je wajen wani mai tireda, ya nuna karamar jikkar omon ‘Good Mama’ ya ce a ba shi jikka daya. Shi ya zaci madarar gari ce ta leda. Ya amsa ya nufi teburin mai shayi, ya samu wuri ya zauna. Ya ce wa mai shayi a zuba masa amma kar a sa madara. Bayan an ba shi ruwan shayi, sai ya dauki kofi daya daban ya zazage farin omon nan, ya zuba ruwan shayi ciki ya fara shekawa. Kafin ka ce kwabo sai kumfa ta cika kofin har tana zuba. Shi kuwa sai ya ce: “Aradu wannan ai fitsarin jaki ne!”

SINASIR NA SEMOVITA

SINASIR NA SEMOVITA Semovita suga yis ruwa gishiri mai zaki kwaba semovitan da yis kamar kwabin fanke sai ki barshi ya tashi kamar 30 min san nan ki dauko kullun ki dan kara masa ruwan sanyi yayi dai dai kullun waina sai ki sa masa dan gishiri da suga ki juya sosai idan kina son albasa zaki iya sawa sai ki dora kaskon suyar sinasir dinki ki fara suyar ki zuba mai sai ki zuba kullun ba a juyawa har ya soyu amma idan kina so zaki iya tunda na semovita ne,shikenan kin gama zaki iyaci da komai.

Yanda ZAKI CAKE

CAKE flawa kwata kwai 7 madara baking powder butter leda 1 sukari gwangwani 1 vanilla ki zuba butter da sukari a cikin mixer su juyu sosai har su narke sai ki fasa kwannan shima ki zubashi duka a ciki yaci gaba da juyawa,ki kawo flawar da kika tankade kika sa mata baking powder kina zubawa har yayi kauri,sai ki zuba madara da vanilla ya juyu sosai,sai ki wanke gwangwanin gasa cake dinki ki shafa masa butter ki zuzzuba kullun a ciki ki gasa.

FRIED CABBAGE

FRIED CABBAGE Cabbege 1 dankali 4 karas 6 nama yadda 1 kilo kwai 5 ko 10 maggi albasa soy souce mai zaki dafa namanki da magi da albasa da citta yadda zaiyi dandano,saiki yayyankashi kanana,saiki fere dankali da karas ki tafasasu saiki soyasu amma daban daban ki ajesu a gefe,ki yanka cabbage girman da kike so amma ya kasance da girmansa,shima ki dan tafasashi,idan ya tafasa sai ki saukeshi ki tsane,ki yanka albasa akai,saiki kawo sauran kayan da kika aje ki zuba akai ki zuba soy souce dan karin dan dano magi da curry da dan gishiri idan kinaso,saiki zuba mai a kasko kamar cokali 4 saiki juye wannan hadin a ciki kiyi ta juyawa har ya hade jikinsa zakiga kwan ya makale a jikinsu sai ki sauke zaki iyaci da lemo. NOTE:-- Nima xanci in kiyi.

EGG & MEAT

Image
EGG & MEAT 1--Kwai 10 2--Nama kilo 1 3--Albasa 2 4--Attaruhu 4 5--Mai 6--Maggi&Gishiri 7--koran tattasai 5 Ki daka namanki da da kika dafa amma mara jijiya,ki jajjaga attaruhu albasa koran tattasai ki hadasu da naman ki cakudasu ki fasa kwai ki kadashi ki juyeshi shima a ciki,zuba magi da gishiri dai dai kima,ki dora mai a wuta idan yayi zafi sai ki soya kamar wainar kwai ko kuma yadda kika gani a hoto (amma me tudu),ana ci da tea ko kunu,"yar uwa idan kin gwada karki manta dani. NOTE:-- Ki tsaya ta bayan mai gidanki kaada ya fadi

KOSAN SEMOVITA

KOSAN SEMOVITA Semovita Kwai Nama ko kifi Albasa Attaruhu Man gyada Maggi & gishiri Yeast Curry zaki kwaba semovitanki da yeas kamar zakiyi fanke kibarshi ya tashi,saiki jajjaga albasa attaru ki aje gefe,san nan ki daka dafaffan namanki ko kifi ki hada dasu attaruhu ki ajiye,ki dafa kwai ki yayyanka sannan ki fasa wani ki ajiye,ki dauko kullun nan ki duba ko ya ttashi idan ya tashi sai ki zuba wadannan kayan duka a ciki tare da curry maggi da gishiri ki juya sosai, sai ki dora mai a kan wuta kamar zakiyi kosai ki dinga diba kina zubawa idan da wutama zakiga yana juyawa dakansa ba sai kin juyaba,sai a kwashe za a iyaci da kunun shinkafa ko na shi semovita din ko kuma wanda kike so,anjima in Allah yaso zamu kawo daya daga ciki.

SHINKAFA DA KWAKWA

SHINKAFA DA KWAKWA -Shinkafa. -Nama. -koren wake. -kayan miya amma banda tumatir. -kwa-kwa. -karas. -maggi,gishiri da sauran su. Da farko zaki tafasa shinkafan ki,ki wanke ki aje a gefe.sai ki zuba mai a tukunya ki zuba namanki a ciki da maggi da gishiri da kayan kamshi ki rufe yadan dahu,sai ki dauko kwakwanki ki kankare bayan ki markada ki tace sai ki zuba ruwan a kan naman nan dake kan wuta ki kara su maggi da su albasa da tattasai da koren waken ki da lawashi,ki rufe ya tafasa waken ya dahu,saiki zuba shinkafan da karas din da kika yayyan ka harya tsotse.ki gwada dan jiyama naci Hmm kada kibawa mai rowa

KUNUN SHINKAFA

KUNUN SHINKAFA Shinkafa gwangwn 2 Madara peak 1 Sukari Kwakwa 1 zaki wanke shinkafarki ki bayar a markado miki ki tace sannan ki bare kwakwarki ki kankare bakin bayanta ki gogata a abin goga {kubewa} amma kanana sai ki dora tukunya a murhu ki zuba ruwa yadda zai yi miki, sai ki kawo kwakwar nan ki zuba a c2iki su tafaso tare idan bakyason citon zaki iya kwashewa amma dashi yafi dadi,saiki kawo kullun nan ki dama kamar kunu,idan kina son lemon tsami zaki iya sa dan kadan,sai ki sa suga da madara ki juye a flas, NOTE:-- Ammafa akwai dadi sosai

FRIED RICE

FRIED RICE Shinkafa nama karas hanta koran wake koran tattasai attaruhu albasa kabej mai magi&gishiri curry zaki dafa nama da hanta ki yankasu kanana ki yanka kayan lambun suma kanana,ki dora ruwan shinkafa ya tafasa sai ki zubata,idan tayi rabin dahuwa sai ki sauke ki taceta,ki dora manki a wuta ki zuba kayan nan da kika yanka tare da albasa da attaruhu da kika jajjaga,kiyi ta juyawa har suyi laushi,sai ki zuba shinkafa da nama gishiri magi curry kiyi ta juyawa har tayi warara,kayan lambun zasu fito sosai,idan kina son ruwa zaki iya dan karawa.

ALKUBUS

ALKUBUS Alkama Fulawa Yist Kanwa Gishiri Mai zaki tankade garin alkama da fulawa ki hadasu waje daya ki jika yis ki saka dan gishiri ki kwaba yafi kwabin fanke tauri ki rufe zuwa ya kumburo sai ki dan disa mai da yar kanwa kiyi ta bugawa ya bugu sai ki dauko kana nan kwanuka ki shafa mai a ciki ki zuba ki turarashi ko ki zuba a leda ki kullashi kamar alala ki dafashi,za a iyaci da romo ko miyar taushe ko ta agush.

ME NENE BURIKA BARI KAJI

Burin Mata - AURE. Burin Maza. - JOB. Burin yara. - WASA. Burin Tsoffi. - HUTU. Burin bakano.- Tara kudi ko halal ko haram. Burin. Bakatsine.- Yasha SIGARI. Burin Bazazzagi.- Yayi MATA 4. Burin. Ba sakkwace- kashema mace kudi. Burin bahadeje.- yaje YAKI. Burin inyamiri- yayi 419. Burin beyarbe- yayi MUNAFUNCIi. Burin bafilatani- yaje KIW0. Burin bahaushe.- yayi AURE. Burin bakatafe- yashe BURKUTU. Burin dan PDP- yayi Magudin ZABE. Burin dan APC- BUHARI yaci ZABE. Burin wanda yaturo wannan - sakon buhari ko kwankwaso yaci zabe. Burin duk wanda ya karanta wannan sakon gudluck ebele jonatha ya sauka mulki. Ya Allah ka kare mana yan uwanmu musulmai a duk inda suke. Kadauka addinin musulunci ka tarwasa duk wani wanda yakeso yaga bayan addininka dan Alfarman annabinka muhammed (s.a.w).

AIRTEL USERS

Sannunku abokai kamar yadda kuka sani da layin airtel suna bada kyautar mb daga 50 zuwa 100 kai har 200 to amma abin dubawa anan shine kowa yasan da ba kowane sim suke bawaba to amma yanxu ko wanne suna bashi idan da ka taba yi ba ka samu daceba to yanxu ka han xarta ka dauko sim dinka ka gwada kawai ka danna 141 13*200# xaka samu 200mb idan kuma basu baku wannan ba to kayi mai haka 141 13*100# shima idan basu bakuba to jarraba wannan 141 13*50# na tabbata insha allahu xaku samu idan kuma har baku samuba to kuyi hakuri dama kyautane kuma sai mai rabo nide nayi sa,a wlh na samu 200mb kuma yanxu haka da ita nake amfani kuma nayiwa mutane da yawa duk kuma sun samu Allah ya bada sa,a

Mobile Phones and Tablets Data Plan Plan

Mobile Phones and Tablets Data Plan Plan Name Amount Data Cap Validity SMS to 131 Targeted Device MTN Mobile Daily #100 10MB 24 Hours 104 Handset MTN Daily Internet #500 150MB 24 Hours 104 Handset/ PC/ Tablet MTN 250MB Mobile Browsing #1,300 250MB 24/7 / 30Days 109 Handset/ PC/ Tablet MTN 500MB Mobile Browsing #2,000 500MB 24/7 / 30Days 110 Handset/ PC/ Tablet MTN 1GB Mobile Browsing #3,500 1GB 24/7 / 30Days 111 PC/ Tablet MTN Monthly For Mobile #1000 100MB 24/7 / 30Days 106 Handset MTN Weekly For Mobile #500 25MB 7Days 105 Handset MTN Monthly Internet #8,000 5GB 30Days 101 PC/ Tablet MTN Weekend Internet #3,000 3GB 9am Fri-9pm Mon, 30 Days 108 Handset/ PC/ Tablet MTN Day Time Internet #6,000 3GB 9am-9pm 30 Days 107 Handset/ PC/ Tablet MTN Night Internet N2,500 3GB 9pm-6am 30 Days 102 PC/ Tablet -------------------------------------------------------- MTN Hourly Plans Time Limit Amount SMS to 131 Validity Period 2 Hours #250 2H 2 Days 20 Hours #1,500 20H 7 Days 100 Hours #5,000 100H 30...

MTN ZONE KAWAI

Image
Aboki ga garabasa amma idan kana afani da MTN ZONE plane don kiran wani layin da ba mtn ba kuma suyi charge kamar kana mtn zone. Kawai kara number da zakai kira, misali glo ce 08055664477 Ku kwada ku bani labari

MTN ZONE KAWAI

Image
Aboki ga garabasa amma idan kana afani da MTN ZONE plane don kiran wani layin da ba mtn ba kuma suyi charge kamar kana mtn zone. Kawai kara number da zakai kira, misali glo ce 08055664477 Ku kwada ku bani labari

HANYOYI 21 DA ZAKA RAGEWA ANDROID PHONE JAN CAJI DA CIN DATA

HANYOYI 21 DA ZAKA RAGEWA ANDROID PHONE JAN CAJI DA CIN DATA Kamar yadda kuka sani Android ba kamar sauran wayoyi bane, domin ita an tsarata da manyan abubuwa, sannan da yawan application wannan tasa masu ita suke ta kuka da ita wajen jan chaji da jan data, to ga wasu hanyoyi da zaka rage mata jan chaji na batir dinta. 1. Ka bude"Menu"sanna n ka nufi"Setting"sa ika latsa"developer 's options"sannan ka tafi can kasa, domin duk wani seti na wayar yana wurin saika latsa" Background process limit"zaka ganshi yana"standard limit"wato bashida adadin yawan app da wayar zata bude lokaci daya, to amma saika takaita, misali ta rika bude guda biyu, sabanin da wajen goma suna budewa suna aiki. Wannan zaisa batir naka yayi kwari, amma wannan baduk android keda wannan ba sai dai version 4.0. Bayan ka seta wannan kayi restart na android naka, domin ta fara aikinta nan take. 2. Ka rika rufe bluetooth naka, kuma ya rika zama a hide, duk da android t...

KOSAN NAMA DA KWAI

KOSAN NAMA DA KWAI Kayan hadi:- •Wake •Fulawa •Kwai •Albasa •Attarugu •Maggi Gishiri, thyme, curry •Man gyada. Ki wanke waken ki, ki cire dusar a kai a markado miki kamar markaden kosai, amma ki zuba attarugu da albasa a waken kafin ki kai niqan, sannan albasan ce zaki sa dayawa attarugun kuma dan dai-dai, idan wake gwangwani hudu kika sa sai kisa fulawa gwangwani daya, a kan markadadden waken, sannan ki tafasa naman ki ya tafasu sosai, sai ki sa a blender ki niqa ko kisa a turmi mai kyau ki daka. Sannan ki kada danyen kwai, kamar guda hudu ko uku ki zuba a kai, sannan ki sa Maggi, gishiri, da curry da thyme yadda zai ji, sai ki buga shi sosai, sai ki dora mai dinki a wuta idan yayi zafi sai ki dinga soyawa kamar yadda zaki soya kosai. Tun kafin ki gama qamshi zaki ji yana tashi, kunnin maigida kuma sai yayi motsi. Nasan wasu zasu tambaya ko da me za'a ci? Za a iya ci da Koko, kunun tsamiya, kunun gyada, kunun acca, ko ma asha da shayi, kuma za'a iya cin shi zalla

DARASI! DARASI!! DARASI!!!

DARASI! Wani attajirin me kudi da ya shagaltu da duniya, domin duk wata bushasha ta duniya dashi ake damawa. Watarana, sai ya kira me kula da gidan shi wato (Me-Gadi), sai ya bashi wani kullin abu a leda yace dashi "gashi ka ajiye, idan ka hadu da wanda yafi kowa sakarci (Sakarai) sai ka bashi. Nan take ya amsa ya kuma adana shi kamar yadda aka bashi umarni, a kwana a tashi, bayan wasu shekaru sai wannan attajirin ya kamu da rashin lafiya, wanda ta kai da kyar ake ganin zai rayu. Sai wannan bawan Allah me kula da gidan nashi (Me-Gadi) yazo duba shi asibiti, bayan ya gama yi masa jaje, sai wannan me gida nashi (Attajiri) yace dashi "ni ina ganin kwanaki na sunzo karshe, domin wannan jinya tawa bata tashi bace" Me-gadi ya kada baki ya tambaye shi... *Shin ka tanadarwa kanka babban gida a can kamar yadda ka gina katafaren gida a nan duniya me AC, Lantarki, Pool, Intanet,? Attajiri yayi shiru. *Shin ka tanadawa kanka Motocin hawa kamar yadda ka tara su a nan duniya? Attajiri...

kuduba wannan girma

Akwai Wata Mace Karuwa Marar Kunya a Cikin Garin Madeena. Watarana Ta Zo Wucewa Kusa Da Inda Sayyiduna RASULULLAH(S.A.W) Yake Zaune Tare Da Sahabbansa Suna Cin Nama, Sai Tace:- "DON ALLAH KU BANI NAMAN NAN INCI" Har Sun Taso Zasu Miko Mata, Sai Ta Ce:- "NI NA CIKIN BAKIN MANZON ALLAH(S.A.W) NAKE SO". Shi Kenan Sai Sayyiduna RASULULLAHI(S.A.W) Ya Tattauna Naman a Cikin Bakinsa Mai Albarka Sannan Ya Mika Mata, Ta Karba Ta Cinye. Tun Daga Wannan Ranar Sai Halayenta Suka Sauya, Ta Zama Salihar Mace Mai Kamun-Kai. Nan Da Nan Ta Ji Wata Irin Kunya Ta Lullubeta. Tun Daga Wannan Ranar Bata Qara Yin Zina Ba, Ko Zancen Batsa Bata Qara Yi Ba. ALBARKACIN YAWUN MANZON ALLAH(S.A.W). Ya ALLAH Kayi Salati Da Aminci a Gare Shi Gwargwadon Darajarsa. Tare Da Iyalan Gidansa Da Dukkan Sahabbansa Masu Albarka, Ameen.

SAKI UKU A DAREN AMARCI

SAKI UKU A DAREN AMARCI Wani matashi ne Allah ya azurta shi da ilimi zamani da kuma na addini, ga kuma Allah ya bashi arziki dai-dai misali. Sai yanke shawarar yin #Aure, kuma Allah ya hada shi da wata baiwar #Allah da ta kwanta masa a zuciyarsa. Nan take ya mika mata uzurinsa, tayi amanna dashi, kuma ta karbeshi hannu bibiyu. Ba da dadewa ba, aka sanya musu ranar auren su. Lokaci yayi aka daura musu aure, sai dai ba'anan gizo ke sakar ba. Bayan ansha biki an watse, sai abokanan ango suka raka shi gidansa, kuma sukayi ban-kwana dashi. Cikin dare, sai makwabta sukaji #Amarya tana rangada #ihu, tana cewa yanzu saki na kayi? Nan take #Makwabta suka shigo domin kawo dauki bisa abinda #Amaryar take fada. Shigarsu gidan, sai sukaji #Angon yana cewa "Na sake ki saki uku (3), kuma ba zaki kwana a gidana ba" Shike nan, wannan makwabtan suka dauke ta suka kaita ta-kwana a wajensu. Da safe sukace da ita ta tafi wajen iyayenta ta fada musu halin da ake ciki. Bayan tazo gida ta fadawa...

matsala na da mata

Darajarki Da Mutuncinki Yana Hannunki! Yake 'Yar uwa, ki sani cewa Jan-Aji Kinibibi, ko kuma Takama ba zai taba kawo miki shakuwa azuciyar masoyinki ba. 'Yan mata zaku ga maza nata bibiyarku domin su ga sun aure ku, zasu bi duk wata hanya domin kun zama matansu na Sunnah. Amma sai kaga ke mace kina juya shi wai domin yazo yace yana Sonki. Jan-aji, Takama, Kinibibi, Ji-da-Kayi. Ki sani cewa duk wannan huduba ce ta Shaidan La'ananne, wanda daga karshe zai kai ne ya baro kawai, daga baya ki fada dana sani wanda keya ce. Sai kaga mace ta sami me Sonta tsakani da Allah, wanda zai nuna mata tsabtatatciyar Soyayya, ya baki kulawa, yaso yaga ya faranta miki, yayi alfahari dake, amma sai kaga ke mace kina juya shi domin kinsan yana Sonki. Koda ke kina sonshi, amma sai muggan kawaye suna baki gurguwar shawarar da zaki fada ramin da babu damar fitowa, wannan kawaye da kikaga suna baki wannan shawara na ki juya masoyinki yadda kike so, ki tambaye shi kudi ko kuma wani abu da har zai je...

LABARIN WANI SAURAYI

Wani matashi ne ya tashi da akidar rashin son Aure har sai yayi kudi. Allah da ikonsa ya baiwa matashin damar yin karatun Boko har ya kai Dakta ba tare da ya yi Aure ba, ya kuma samu aiki, sannan ya fara batun neman Matar da zai Aura. Ana haka, sai Allah ya hada shi da wata Kyakkyawar Yarinya mai hankali da fahimta, sai dai ta fi shi ilimin Addinin musulunci, suka yi Aure aka tare, amma shi Ogan baya son ayi saurin haihuwa, matar kuma sai kokarin fahimtar da shi illar yin hakan amma inaa, ya yi nisa baya jin kira. Mutumin nan ya rinka baiwa Matarsa magungunan hana haihuwa, haka kuma suka kwashe shekaru 5 zuwa 6 ba tare da an samu albarkar Aure ba, Iyayensa da na Matar kuwa sai kokawa suke. Wata rana da kansa ya cewa matar shi nadai yana sha'awar karamin Yaro, amma Namiji ba Mace ba. To lokacin da Allah ya baiwa matar ciki, sai yayi ta jin dadi, amma yana gaya mata fa, ta tabbatar an samu Daa Namiji, a haka dai ta haifi 'ya Mace bisa yadda Allah ya kaddara, ya kuma rinka kyamar ...

WACCE SHIGA YA KAMATA KIYI A GIDANKI.....

WACCE SHIGA YA KAMATA KIYI A GIDANKI..... 'Yar uwa kizama meyin dressing kala-kala karki nacewa kwaya daya.... Kullum english dress kamar wata ba saban ba, a'a karkade kunnen ki kiji... Yau in kika zama baturiya, To gobe kizama balarabiya a wajen dressing.... Jibi kuwa nemo pakistan dinki damammu kisa kizama indiya... Shigar hausa kuwa karki bari a barki a baya don yanzu akwai dunkuna damammu na daukar hankalin mai gidanki... Gata kuwa ki canja kizama beyarabiya, Yi kokari kiyita rikida kamar wahainiya..... Kullum kita bashi mamaki, bawai dressing daya ba wanda kullum zai shedaki dasu... Ko tunaninki ki zaiyi da wannan shigar zai ganki a kwakwalwarsa saboda ita yake gani kullum.... Karki bari Ogah ya fita yaga wata da shigar dake bakyayi har yayi mata kallon da bana shari'a ba.... 'Yar Uwa Bude Idonki Karki Bari A Barki A Baya...

KAWAR MATATA..1

KAWAR MATATA..1 Zaune nake ina karatun jarida Daily trust da yake week end ne yau ba aiki ina gida ina hutawa da iyalina, "salamu alaikum"....akarafka sallama daga bakin kofar falon.., Ban amsa ba kaman yanda ban dago kai daga karatun da ya daukemun hankali ba, matata Safna dake goge gogen falon nesa dani kadan ta dago kai tare da sakin wani dan ihu da ke nuna tsananin murna, "labiba kece yau a gidanmu ikon Allah ashe zamu sake ganawa dake" safna ta tambayi wanda ta kira da labiba... tare da sakin abun goge gogen ta rungumeta... "banyi zaton zamu sake haduwa ba labiba a tsammanina ma kin manta dani ne" Safna ta fada bayan sun saki juna....labiba ta dubi safna tana murmushi tace "wallahi kawata ina nan aminci bazai sa na manta dake ba kinsan Daddy dina anmai canjin wajen aiki zuwa malesia embassy to can muka koma kuma anan aka samarmun admision yanzu ma na gama digrina amma kina raina wallahi ina maigidan naki?" Labiba ta tambaya,....da sauri safn...

TARIHIN SARKIN KANO MUHAMMAD RUMFA DAN YAKUBU kashi na farko

TARIHIN SARKIN KANO MUHAMMAD RUMFA DAN YAKUBU kashi na farko Rumfa sarki ne da babu kama tasa gama kirarinsa- balaraben sarki ya gyara kasa A zamaninsa yaki ya auku tsakanin kanawa da katsinawa shekara goma sha daya babu wanda yai rinjaye sarki rumfa shine ya fara abu .2 cikin wannan kasa 1 ya gina gidan nan da ake cewa gidan rumfa sa,ad da shekara ta gewayo ya kara birni tun daga kofar dagaci zuwa kofar mata zuwa kofar gyarta wasa zuwa kofar kawaye zuwa kofar na,isa zuwa kofar kansakali da shekara ta komo ya gina gidansa shine ya kafa KASUWAR KURMI, kuma ya fara dawakin zage domin yakin katsina, shine yafara mallakar mace dubu, shine wanda ya fara kulle,ya fara tara dabo da kakaki da takalman jimina da figini shine ya fara sallar idi a sha da koko shine ya fara baiwa babanni sarauta, mu hadu a kashi na biyu

WASIYYAN UBA CIKIN HIKIMA.

WASIYYAN UBA CIKIN HIKIMA. Wani mutum ne yana bisa gadon asibiti yazo gangaran mutuwa sai yacewa dansa,"yaa dana naso nayi maka wasu nasihu guda hudu,amma bazan samu yi maka su yanzu ba sbd nasan mutuwa zanyi,abinda nakeso da kai idan na mutu kaje wajen TSOHON DOKI da KARE da KIYASHI da MESA(maciji) kafada musu na aiko ka suyi maka nasiha za suyi fada abinda nakeso na fada maka. Yana gama fadawa dan nasa haka ya cika da karman shada. Dan yai kuka sosai, bayan anyi sadakan uku sai dan ya tashi ya tafi wajen TSOHON DOKI yace"babane kafin ya mutu yace idan ya mutu nazo wajenka da KARE da KIYASHI da MESA wai zakumin nasiha. Tsohon doki yace,"lallai mahaifinka yayi gaskiya,abinda yakeso ya fada maka wanda yace kazo na fada maka shine,duk abinda zakayi kayishi cikin kuriciyarka kayishi akan lokaci kada ka bari lokaci ya kure maka bakai ba,kaganni lokacin ina saurayi da karfina ana kawomin abinci akan kari,ana min wanka kullum, ana sharemin wajen kwanciyana, ammayanzu dana tsuf...

Labarin Yaro da Kunama

Labarin Yaro da Kunama An yi wani lokaci akwai wani yaro marar ji, duk abin da aka fada masa ba ya saurarar mutane. Ya cika rigima, komai ya gani sai ya taba, ko kuma ya lalata. Mahaifiyarsa babu irin nasihar da ba ta yi masa amma ya ki ji, wani lokaci har ta lakata masa duka amma hakan ba zai hana ya ci gaba da rashin jinsa ba. “Idan ba ka daina rashin ji ba, wata rana za ka hadu da gabanka, a lokacin za ka dandana kudarka, za ka kuma fahimci lallai rashin ji ba shi da amfani.” Inji mahaifiyarsa wata rana tana yi masa nasiha. Amma bai saurare ta ba, ya fita waje yana guna-gunin ana takura masa. Wata rana ya zo zai sanya takalminsa, sai mahaifiyarsa ta ce masa ya zazzage takalminsa, sannan ya share kafarsa kafin ya sanya takalmin, amma ya yi kamar bai ji ta ba, zai sanya takalmin ke nan ta sake fada masa, amma ya ki bin umarnin da ta yi masa. Ashe abin da bai sani ba shi ne, akwai kunama a cikin takalmin, bayan ya sanya ne ta harbe shi, a nan ya rika kuka, hankalin mahaifiyarsa ya tash...

Dan Takarar Gwamna Ya Fice Daga Jam’iyyarsa Ana Tsaka Da Zaben Fidda Gwani

Dan Takarar Gwamna Ya Fice Daga Jam’iyyarsa Ana Tsaka Da Zaben Fidda Gwani Wani dan takarar gwamna a daya daga cikin jam’iyyu masu san tsaida dan takarar gwamna a jihar Kano ya fice daga jam’iyyarsa ana tsaka da zaben fidda da gwani da jam’iyyun kasar nan ke yi a yanzu ciki kuwa har da jam’iyyar APC, PDP, PDM, DPP, LP. da dai sauran jam’iyyu sama (50) wanda hukumar zabe INEC ta yi wa rijista domin fafatawa a zaben gama gari da za a gudanar a 2015. Jam’iyyar LP da ke da magoya baya a jihar Kano yanzu haka dan takarar Gwamnanta, Barista Tijjani Muhammad Yakasai ya fice daga jam’iyyar inda ya koma jam’iyyar DPP anan take.

AN TAMBAYI MALA'IKAN MUTUWA.

AN TAMBAYI MALA'IKAN MUTUWA. Baka taba yin kuka ba sanda kake cire ran dan Adam? - Sai ya amsa, nayi kuka sau daya, nayi dariya sau daya, kuma naji tsoro sau daya.. - Ubangiji yace: Menene yabaka dariya..? sai yace wani mutum ne naje daukan ransa, shi kuma yana fadawa mai dinka masa takalmi... kayishi mai kyau yanda zanyi shekara ina sawa, sai na dauki ransa ba tare da yasa takalmin ba... -Ubangiji yace:menene yasaka kuka? yace sanda ka aikeni dauko ran matarnan a sahara, bayan ta haifi danta a lokacin sai nayi kuka saboda ihun da dan yakeyi ba mai taimakonshi... -Ubangiji yace: Menene yabaka tsoro? yace sanda ka aikeni in dauko ran wani malami, duk sanda nakusanci dakinsa haskene yake dawo dani, hasken ransa ya tsoratar dani sanda nazo cireshi... -UBANGIJI YACE MASA KASAN WAYE WANNAN MALAMIN.. .???YACE A'A.... -Yace wannan yaronne daka dauki ran mahaifiyarsa a sahara, Ni Na jibinci lamarinsa ban barshi a hannun kowa ba....!!! ALLAHU AKBAR. . Dan uwa ko yar uwa mu mika lamurran...

SU WAYE......MATA ?

SU WAYE......MATA ? Kalmar MACE tamkar (GOLD) ne ko kuma muce Sinadarin ZINARI mai yin WALKIYA akowane LOKACI, ~MATA, Sunada wani SINADARI na Farin JiNi wanda yake da matukar Tasiri a idon MAZAJE, ~MATA, Sunada matukar kima a Cikin Al'Ummah wadda har takai ga sun samu martaba da matsayi Babbah, ~MATA, Sunada wani LAUNI mai Juya MAZAJE, Tamkar Limzamin DOKI har ya kai ga komai MATSAYINKA, MULKI, KUDI ko SARAUTA.MACE sai ta Juya ka, ~MATA, Sun Amsa Sunan Su MATA ga jan AJI da Juyin Juya Hali, komai Rashin Kyan. MACE Kalma daya Zata sa KASO ta nanTake, ~MATA, Sunada Hikima da Jurewa akan abunda suke matukar SO, amman sai sukasa Nunawa, ~MATA, Sunada Kunya, Hakuri da Juriya har sukan burgeka idan Ka Iya Zama Dasu, ~MATA, Basu son mai kuntata masu koda yaushe sunfi son Mai kyauta ta masu, ~MATA, Suna son RAHA da Abun DARIYA ko kuma Nishadantarwa, ~MATA, Zuciyar su FARA ce tamkar farin RUWA ba wuya shawo kansu idan ransu ya Baci, ~MATA, Sunada HAKURI da Tausayi da kuma Firgita akan wani ...