TUN KAFIN ZUWAN MUSULUMCI
1)Tun kafin zuwan Musulunci Mushirikkan Makkah suna azumin ashura, Annabi SAW ma ya azumce shi a Makkah ( Bukhari) 2) Da Annabi SAW yayi hijira zuwa Madinah ya sami Yahudawa a Madinah suna azumtar shi ya azumce shi ya umurci Musulmi su azumce shi (Bukhari) 3) Annabi SAW yace game da azumin Ashurah ina tsammanin Allah ya karkare zunubban shekarar da ta wuce (Muslim) 4) Yace : idan na rayu zuwa shekara mai zuwa zan azumci tara gawata (Muslim) 5) Azumi kawai aka sani a lokacin Annabi SAW da Abubakar da Umar da Usman da Ali da Muawiya Allah yayarda da su. Daga baya yan shia suka kashe Husaini a Karbala ranar ashura sai mutane suka kasu uku: (a) Yan shiar da suka kashe shi suka riki ranar ranar makoki da bakinciki (b) Nawasib suka rike ta ranar murna da cika ciki (c) Ahlussunnah suka cigaba da azumi kamar yadda ya tabbata a lokacin Annabi SAW. 6) Don haka duk Hadissan da sukazo gameda falalar cika ciki basu inganta ba (Tamamul Minnah) 7) Tara ga wata (Tasu'ah) zai kasance Lahadi goma ga...