ALBARKACIN HANNAYEN ANNABI (SAWW).

SAYYIDUNA ABU-HURAIRA (RTA) YACE:

"Watarana nazo wajen Manzon Allah (saww) da wani dabino dan kadan, Sai nace Masa :

"YA RASULALLAHI YI MIN ADDU'A MANA, KA ROQA MIN ALBARKA ACIKIN WANNAN DABINON NAWA"

Sai ya kar'ba, ya sanya shi atsakanin hannuwansa, sannan yayi addu'a.

Sannan yace min: "KAR'BI, KA SANYA SHI ACIKIN JAKAR DA KAKE ZUBA GUZURINKA ACIKI. KUMA DUK LOKACIN DA ZAKA CI DABINON, KA SANYA HANNUNKA KA DEBO DAGA CIKIN JAKAR, AMMA KAR KA JUYE".

Sai nace "to".

"Wallahi Sai da na rika ciyar da mutane masu yawa, kuma ina yin sadaqah daga cikin wannan dabinon..
Kullum aciki nake ci nake sha. Ban ta'ba rabuwa da wannan jakar ba. Duk inda zanje tana nan a kwuibi na."

Na ci-gaba da cin Wannan dabino (Babu yankewa, babu Qarewa), Har Manzon Allah (saww) yayi wafati, Har Tsawon lokacin Khalifancin Sayyiduna Abubakar Da Sayyiduna Umar, da Sayyiduna Uthman. (Allah ya yarda dasu)"

Yayin da Aka kashe Sayyiduna Uthman (ra), Sai jakar ta Fadi daga Hannu-na." (Tsawon SAMA DA SHEKARA ASHIRIN KENAN).

"Shin kuna so in gaya muku ko buhu nawa na fitar naci daga cikin Wannan jaka?"

"WALLAHI NA CI SAMA DA BUHU DARI BIYU".

AWATA RUWAYAR KUMA, ABU HURAIRA (rta) yace:

"Wata rana (awajen yaki) Manzon Allah (saww) yace min

"KIRA MIN MUTUM GOMA"

Sai naje na kira su, Suka ci, Suka ci sai da suka Qoshi, Sannan yace In Sake kiran wasu Mutum goma din, su ma suka ci, Suka ci sai da suka Qoshi. Da haka Sai da Gaba dayan rundunar Kowa yaci dabinon nan ya Qoshi, Amma Dabinon yana nan kamar yadda yake tun farko" (BAI RAGU BA).

A WATA RUWAYAR KUMA YACE:

"MUSIBU GUDA UKU NE SUKA TA'BA SAMU NA AMUSULUNCI WADANDA BABU KAMARSU:

1. WAFATIN MANZON ALLAH (SAWW).
2. KISAN SAYYIDUNA UTHMANU.
3. FADUWAR WANNAN JAKA".

★ hadisai ne ingantattu, aduba musnad na Imamu
Ahmad bn Hambal, juzu'i na 2, shafi na 352.

★ Tirmidhy ma ya kawo shi acikin Manaqibu abu
huraira.

★ Sannan Imamul Baihaqy ma ya kawo shi acikin
Dala'ilun Nubuwwah, Juzu'i na 6, Shafi na 110
zuwa na 111.

Comments

Popular posts from this blog

SUNAYEN SAHABBAN ANNABI (S.A.W) GUDA GOMA WA "YANDA SUKA MUTU DA CERTIFICATE NA SHIGA ALJANNAH

FARILLAN SALLAH

MTN BONANZA