Jihar Jigawa Zata Goyi Bayan Shugaba Jonathan A 2015- Walin Dutse
A firar da yayi da wakilin Muryar Amurka Mahmud Ibrahim Kwari, Alhaji Bashir Dalhatu, Walin Dutse yace ya gana da shugaba Jonathan kuma zasu goyi bayansa domin ya nunawa jihar da mutanenta kauna.
Alhaji Bashir Dalhatu yace ya fadawa shugaban kasa cewa ya ziyarci jihar kaman sau hudu ke nan tunda ya kama mulki abun da ya nuna cewa yana kaunar jihar.
Duk lokancin da ya zo jihar yana yi masu alkawura kuma yana cikasu. Ya yiwa jihar ayyuka. Misali ya gina makarantu da jami'a da tituna da bunkasa ayyukan harkokin noma da kuma sabon filin saukar jiragen sama da ma wasu abubuwa da dama dake kara inganta jihar.
Alhaji Bashir Dalhatu yace ya fadawa shugaban kasa cewa ya ziyarci jihar kaman sau hudu ke nan tunda ya kama mulki abun da ya nuna cewa yana kaunar jihar.
Duk lokancin da ya zo jihar yana yi masu alkawura kuma yana cikasu. Ya yiwa jihar ayyuka. Misali ya gina makarantu da jami'a da tituna da bunkasa ayyukan harkokin noma da kuma sabon filin saukar jiragen sama da ma wasu abubuwa da dama dake kara inganta jihar.
Comments
Post a Comment