AURE A MUSULUNCI
----AURE A MUSULUNCI---- Aure shine hada wata irin alaka tsakanin mace da namiji , wannan yana nufin hade rayuwarsu su zama daya, haka nankuma makomarsu ta zama daya. Kowace irn al’umma akwai irin matsayin da ta bawa aure a musulunci wani dauri ne da yake halattawa ma’aurata {mata Da miji} jin dadi a junansu ta hanyar saduwa da kuma sauran muamaloli ALLAH (SWT) ya halicci mace daga hakarkarin namiji ya kuma sanya soyayya da tausayi a tsakaninsu (kamar yadda yagayamana a alkur’ani mai tsarki ). Wannan yana nun mana cewa alaka tsakanin mace da namiji ALLAH ne ya kulla tun fil’azal. Abin da ALLAH kuwa ya hada babu mai rabawa . wannan shine yasa a dabi’ance kowa ne namiji yana bukatar mace, haka kuma kowace mace tana bukatar namiji. Wato ko wane daya bazai iya wadatuwa dakansa ba, ya rayu shi kasai dole ne sai da wanin sa. ALLAH (SWT) da ya sanya wannan dangatakatsakanin mace da namiji bai barsu haka nan kara zubeba , suyi ta saduwa barkatai ba tare da wani ts...