Malaman Makaranta A Nijeriya Za Su Samu Ilmi Da Gidaje Kyauta, Cewar Osinbajo

Malaman Makaranta A Nijeriya Za Su Samu Ilmi Da Gidaje Kyauta, Cewar Osinbajo

Bincike ya nuna cewa malaman makarantu a Nijeriya za su samu damar karo ilmi kyauta a yayin da jam'iyyar adawa ta APC ta karbi mulki a ran 29 ga wata mai kamawa.

Mataimakin zababben shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo, wanda ya bayyana hakan a yayin wani taro da ya yi da kungiyar malamai ta kasa reshen jihar Lagos a yau, ya kara da cewa ci gaba da karo ilmin Malaman makaranta na daya daga cikin kudirorin gwamnatin APC don ganin ilmin ya habbaka a Nijeriya. Sannan kuma ya tabbatar da cewa za a samarwa Malaman gidajen zama kyauta.

Comments

Popular posts from this blog

FARILLAN SALLAH

BAYANI AKAN JININ HAILA (JININ AL'ADA)

SUNAYEN SAHABBAN ANNABI (S.A.W) GUDA GOMA WA "YANDA SUKA MUTU DA CERTIFICATE NA SHIGA ALJANNAH