Malaman Makaranta A Nijeriya Za Su Samu Ilmi Da Gidaje Kyauta, Cewar Osinbajo

Malaman Makaranta A Nijeriya Za Su Samu Ilmi Da Gidaje Kyauta, Cewar Osinbajo

Bincike ya nuna cewa malaman makarantu a Nijeriya za su samu damar karo ilmi kyauta a yayin da jam'iyyar adawa ta APC ta karbi mulki a ran 29 ga wata mai kamawa.

Mataimakin zababben shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo, wanda ya bayyana hakan a yayin wani taro da ya yi da kungiyar malamai ta kasa reshen jihar Lagos a yau, ya kara da cewa ci gaba da karo ilmin Malaman makaranta na daya daga cikin kudirorin gwamnatin APC don ganin ilmin ya habbaka a Nijeriya. Sannan kuma ya tabbatar da cewa za a samarwa Malaman gidajen zama kyauta.

Comments

Popular posts from this blog

SUNAYEN SAHABBAN ANNABI (S.A.W) GUDA GOMA WA "YANDA SUKA MUTU DA CERTIFICATE NA SHIGA ALJANNAH

FARILLAN SALLAH

MTN BONANZA