Malaman Makaranta A Nijeriya Za Su Samu Ilmi Da Gidaje Kyauta, Cewar Osinbajo
Malaman Makaranta A Nijeriya Za Su Samu Ilmi Da Gidaje Kyauta, Cewar Osinbajo
Bincike ya nuna cewa malaman makarantu a Nijeriya za su samu damar karo ilmi kyauta a yayin da jam'iyyar adawa ta APC ta karbi mulki a ran 29 ga wata mai kamawa.
Mataimakin zababben shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo, wanda ya bayyana hakan a yayin wani taro da ya yi da kungiyar malamai ta kasa reshen jihar Lagos a yau, ya kara da cewa ci gaba da karo ilmin Malaman makaranta na daya daga cikin kudirorin gwamnatin APC don ganin ilmin ya habbaka a Nijeriya. Sannan kuma ya tabbatar da cewa za a samarwa Malaman gidajen zama kyauta.
Bincike ya nuna cewa malaman makarantu a Nijeriya za su samu damar karo ilmi kyauta a yayin da jam'iyyar adawa ta APC ta karbi mulki a ran 29 ga wata mai kamawa.
Mataimakin zababben shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo, wanda ya bayyana hakan a yayin wani taro da ya yi da kungiyar malamai ta kasa reshen jihar Lagos a yau, ya kara da cewa ci gaba da karo ilmin Malaman makaranta na daya daga cikin kudirorin gwamnatin APC don ganin ilmin ya habbaka a Nijeriya. Sannan kuma ya tabbatar da cewa za a samarwa Malaman gidajen zama kyauta.
Comments
Post a Comment