SAURAYI YAFI BUDURWA SANIN KAN TSIYA
Wani saurayi ne yabi wata budurwa akan hanya
yace mata yana sonta ai saurayin nan bai
yi aune ba sai yaji budurwar nan ta sharareshi da mari a fuska har
sai da marin yayi qara mai qarfin da yasa duk mutanen kewayen
wurin suka ji duk suka waigo da sauri inda suka ji qarar, amma
wuf sai saurayin nan ya 'Daga tafin hannunsa sama kamar shine
ya mari budurwar sannan ya 'Daga muryarsa da qarfi yadda duk
mutanen zasu ji yace wa budurwar "idan kika sake bude baki kika
qara cewa kina sona sai na sake gaura maki mari
fiye da wanda nayi maki yanzu"
Sai duk mutanen wurin suka kalli budurwar nan suka fashe mata
da dariya har suna nunata suna cewa "ihu,
yarinya lalle kinsha mari akan soyayya"
Sai budurwar ta dubi mutanen wurin tace
"Wallahi qarya fa ya
keyi, nine fa na mareshi ba shi ya mareni ba"
Amma mutane ba wanda ko ya kulata, kowa sai dariya yake ta
mata kuma ana ba saurayin hakuri akan ya tafi ya kyaleta
hakanan don kada ya sake marinta, da-kyar aka
Lalla6i saurayin ya hakura ya tafi.
Ita kuwa budurwar sai ta fashe da kuka tana fadin
"Allah Ya Isa sharrin da kayi mun"
Haka mutane suka watse suna ta yin mata dariya
suka barta anan tana ta faman rusa kuka.
yace mata yana sonta ai saurayin nan bai
yi aune ba sai yaji budurwar nan ta sharareshi da mari a fuska har
sai da marin yayi qara mai qarfin da yasa duk mutanen kewayen
wurin suka ji duk suka waigo da sauri inda suka ji qarar, amma
wuf sai saurayin nan ya 'Daga tafin hannunsa sama kamar shine
ya mari budurwar sannan ya 'Daga muryarsa da qarfi yadda duk
mutanen zasu ji yace wa budurwar "idan kika sake bude baki kika
qara cewa kina sona sai na sake gaura maki mari
fiye da wanda nayi maki yanzu"
Sai duk mutanen wurin suka kalli budurwar nan suka fashe mata
da dariya har suna nunata suna cewa "ihu,
yarinya lalle kinsha mari akan soyayya"
Sai budurwar ta dubi mutanen wurin tace
"Wallahi qarya fa ya
keyi, nine fa na mareshi ba shi ya mareni ba"
Amma mutane ba wanda ko ya kulata, kowa sai dariya yake ta
mata kuma ana ba saurayin hakuri akan ya tafi ya kyaleta
hakanan don kada ya sake marinta, da-kyar aka
Lalla6i saurayin ya hakura ya tafi.
Ita kuwa budurwar sai ta fashe da kuka tana fadin
"Allah Ya Isa sharrin da kayi mun"
Haka mutane suka watse suna ta yin mata dariya
suka barta anan tana ta faman rusa kuka.
Comments
Post a Comment