Posts

Showing posts from February, 2015

Hanyoyi 10 da za ki bi wajen rabuwa da kurajen ‘pimples’

Hanyoyi 10 da za ki bi wajen rabuwa da kurajen ‘pimples’ Assalamu alaikum, barkanmu da sake saduwa a wannan fili Na samu sakonni mata da yawa da suka nemi na yi bayanin yadda za su rabu da kurajen ‘pimples’. Duk da na ta taba gabatar da irin wannan bayanin, amma sakamakon neman da mutane suka yi na ga dacewar maimaitawa. Ga bayanin hanyoyin da za ki bi wajen rabuwa da kurajen ‘pimples’: (1) Da farko ana so awa biyu ko uku kafin ki kwanta barci sai ki shafa man goge baki a fuskarki, musamman wuraren da kurajen pimples suke da yawa. Ba kowane irin man goge baki za ki shafa ba, ana so ki shafa farin man goge baki ne. Idan kin ga dama za ki iya wanke fuskarki idan man goge bakin da kika shafa ya kai minti 30, idan kin ga dama kuma za ki iya kwantawa da shi har zuwa wayewar gari. Za ki rika maimata hakan har zuwa wadansu kwanaki, idan kin yi hakan za ki ga canji a fuskarki. (2) Ki kasance mai yawan shan ruwa. Yana da kyau duk inda za ki je ki sanya ruwa a Cikin jakarki ba wai dole sai kayan...

kuduba wannan soyayyar ta abubakar A

kuduba wannan soyayyar Wata rana wani mutum yazo wajen manzon Allah ( s a w) yace ya rasulillahi matata ta haihu Kuma gobene ranar da zan radawa jinjirin suna amma banida dabbar da zan yanka masa Kataimakeni kabani dabba daya ina son nabiya bukatata" Sai annabi ( s a w ) yace" kaje gurin Abubakar kace nace yabaka dabbar da zakayi suna daita" Sai mutumin nan yatashi aka nuna masa gidan Sahabi Abubakar dama baisan Abubakar ba yaje yatarar dawani mutum akofar wani gida yanabawa dabbobinsa abinci sai yawuce baiyi masa maganaba Dayaje can gaba sai yasake yin tambaya anuna masa gidan Sahabi Abubakar sai akacemasa ai shine Wanda kawuce akofar gida yana bawa dabbobi abinci Sai yadawo yayiwa Abubakar sallama sannan yace" Muhammadurrasulillah yace kabani dabba daya gobe zan yankata domin in sanyawa yaronda na haifa suna" sai Abubakar yace me kace??? Sai mutumin yafadi abinda yafada masa dafarko sai abubakar yakara cemasa me kace??? Said mutumin nan ya fusata yace wlh ida...

TARIHIN KANO A Takaice

Image
Kano sunan babbar kasar Hausa ce kuma masarauta ce mai kwarjini a cikin kasashen Hausa da kewaye. Haka kuma Kano gari ne babba wanda ya kunshi kabilu masu yawa tare da harkokin arziki. Gari ne mai manya manya malamai kamar su mallam Nasiru Kabara,Shehu Abubakar Atiku,Shek Ja'afar Mahmud Adam. Sanna Garine Mai tarin Ya'nkasuwa kamar su Aliko Dan Gote,Aminu Alhasan Dantata,Mallam Isyaka Rabi'u da dai sauran su. Yawan mutanen da suke garin Kano yakai kimanin mutane Miliyan Goma (10,000,000) a kidayar da aka yi a shekara ta 2006. Kano tana da matukar tasiri a yawan mutane a Najeriya, saboda ita ce ta fi kowace jiha yawan mutane a Najeriya. Idan ka zo Kano za ka samu mutane daga ko'ina a fadin duniya, tun daga na kudancin Najeriya, zuwa kasashen dake makwabtaka da Najeriya, haka kuma za ka tarar da mutanen Sin, da kuma na kasashen Larabawa kamar Sudan, Misira (Egypt), Lebanon, da kuma mutanen kasashen Turai. Kano ta yi suna wajen kasuwancin da ta bunkasa a kai, har ya zamana...

ORANGE APPLE AND CARROT SMOOTHIE

Image
ORANGE APPLE AND CARROT SMOOTHIE INGREDIENTS: »Apple 1 »Orange 1 »Carrot 2 PROCEDURE: Ki fere orange dinki, idan baki son kwalleyen zaki iya tsagawa don ki ragye su, daga nan sai ki kankare carrots dinki, idan blender dinki ba mai karfi bane, to ki yi grating before ki zuba a blender, sannan shima apple dinki ki yayyanka shi, sai ki zuba ruwa mai sanyi dan kadan, daga nan sai ki barsu su nuku sosai. Idan kina so zaki iya sanya sugar ki juye Idan kin sha zaki bani labari.

KAZA ME SHINKAFA

KAZA ME SHINKAFA ¤Kaza ¤Shinkafa ¤Bota ¤Curry ¤Green pies ¤Karas ¤Cabbage ¤Pies ¤Kayan miya ¤Zare da allura ¤Mai Kisami shinkafarki da kika fara dafawa tayi rabin dahuwa,wato da garas garas dinta ki zuba a kwano kiyanka green pies da karas da cabbage, kizuba pies kiyanka attaruhu da dafaffen kwai kizuba maggi, curry, gishiri,kizuba man gyada kadan kijuya shinkafan da wannan kayan da kika zuba.to dama kin wanke kazarki kin cire kai da kafa da kayan ciki kinshafe Kazan da maggi da kayan kamshi,da attaruhu da kika jajjage da curry,sannan ki shafebayanta da bota,kizuba shinkafar da kika hada a cikin zakar sai ki Sa zare da allura ki dinke cikin kazar amma allura sabuwa zaren ma sabo. Idan kin dinke sai kisa kisa a oven ki gasa.

banana drink

BANANA DRINK *Banana *milk *sugar *flavour ki bare ayabanki kiyi blending a blender sai ki dan kara ruwa sabida zaiyi kauri sai ki sa madara,sugar da flavour.sai kisa a friged yayi sanyi haba sai sha

BB

1. Blackberry Enterprise: BB Enterprise yana daya daga cikin manyan feature na blackberry, wanda zaka sanya email dinka akan waya tayi synchronizing din contacts dinka da messages dinka na email, zaka samu saqon email akan wayar ka ta blackberry Kaman yadda kake samun saqon Text Message. Zaka iya saita wannan Enterprise din ne idan ka danna setup a cikin all apps ka zabi email account, ze baka daman sanya email dinka da password, cikin mintoci kadan zaka ga email dinka suna shigowa… Kuma zatayi backup din Numbers dinka dake kan waya zuwa email dinka, koda ka rasa wayar ka da layi, welcome back bazata zama matsala ba kuma zaka samu duka lambobin ka idan ka sake sanya email dinka akan wata BB. 2. Blackberry Messenger: BBM as of last year itace kadai ta rage dalili da wasu suke amfani da BB, amma android na fara wa se suka ji dama basu fito da wannan tsari ba… Duk da haka BBM ta BB tafi ta android features, domin da ita zaka iya Voice Chat ta wifi, wato kayi chatting da mutum kaman kana w...

Alkwari Na four

ALKAWARI 4 Bayan nafice daga gidan ina cikin tafiya nafara tinani " to waye zai dauki wannan chek dinda na aje, bayan babu wanda yasan nayi ajiya agun?" wani bangaren na xuciyata kuma ya shaidamin "kadai koma kakara dubawa" banyi kasa a guiwa ba wurin juyawa, nadauki hanyarda zata kaini gida a saukake... ina shiga nafara bincika ko ina acikin dakin, ina cikin dubawa ne naga wasu takaddu ajikin bango, dasauri nakarasa, abinda nagani shine yayi silar zubar hawayena batareda nasani ba, chek dinda yasmeen tabani ne amman saidai duk an ciccireshi da alama bera ne yaci rabonsa yabar sauran... Fitowa nayi daga gida nakoma bin gidajen mtane wa anda nasani ina fadamasu matsalata domin su taimakamin, atinanina zan iya hada kudin ta wannan hanyar, amman duk wanda natunkara da wannan maganar sai shima yanufoni da matsalar iyalinsa, haka nayini yawo acikin gari amman ba'asamu abinda ake nema ba... magriba nayi nanufi asibiti bantsaya ko inaba sai wurin likita. Shiga nayi off...

Alkwari Na 3

ALKAWARI 3 babu komai na taimake kane saboda Allah bani bukatar wata godiya daga gareka, nima wata rana zan iya zuwa agunka domin neman taimako". haba haleematu ni ai banida wani abu wanda zaki nema aguna. Na kare maganta tareda yimata kallo wanda yake nuna alamar mamaki "hmm hausawa fa sunce ba'a san inda rana ke faduwa ba" haleematu tafada tana kallona... inkau har akwai abinda zaki nema aguna to na tabbata dakin nema nikuma zanyimaki koma minene.... Ahaka dai mukayi bankwana, sannan tajuya fuskarta ixuwa inda wasu mutane da suke zaune, da alama yan aikin gidan ne, sannan takira " sadam! Sadam!!" har sau biyu, sannan naji wani ya amsa "na am hajiya" tache kakai wannan mutumen a katsina "angama hajiya" yafada atakaiche... Daganan muka dauki hanya muka doshi garin katsina... Bamu zame ko inaba sai unguwar tudun wada, sadam dreba ya saukeni adai dai kofar gidanmu sannan yakada motarsa tareda kugamata wuta.... Ina shiga gida khadija ce nag...

alkawari na 2

ALKAWARI 2 A daren ranar juma'ah bawani bacci nayiba sosai wanda zai ishi idanuwana saboda rigimar danarinka yi da bacci akan bazanyiba shikuma yazo yayiman kane-kane a idanuwa, nikuma gani nake idan nakwanta lokaci bazaiyi gudu ba sosai, nafiso inayi ina duba agogo, shiyasa duk bayan dakika daya ko biyu sai nadaga kaina naduba agogon dake makale ajikin bangon asibitin, haka nakasance bankwanta ba sai wurin karfe 02:30am na dare sakamakon karfina da bacci yaci, shima hakan yanada nasaba ne da ruwan da aka tafka jiya da daddare achikin garin namu na katsina wani sanyi yarinka shigowa tako ina har saida nasanya mayafi na lullube, ina lullubewa shikuma bacci sai yasamu wurin zama a idanuwa na....... Cikin ikon Allah batare da wani bata lokaci ba, gari na wayewa saiga likita yazo yaduba lafiyata tareda bada iznin zamu iya tafiya gida yanxu saboda ansamu abinda akeso, dadi da murna aguna abin ba'a magana, tamkar wanda akaba kyautar kujerar makka domin sauke farali. Bayan fitar likit...

ALKAWARI NA 1

ALKAWARI . Part 1. Yunkuri nayi domin intashi amman naji gaba daya nakasa yin komai sakamakon rashin karfin jikina, wani zafi naji a hannuna kamar antsiramin wani abu cikin hanzari nayi sauri na dagashi, sai lokachin nalura da wata allura soke ga hannu na dawata roba doguwa, nanne nabi robar dakallo har inda tushenta yake, abinda idanuwa na suka gani shine yadauremin kai tare da bani mamaki. Ledar jini che nagani arataye, yana biyowa tachikin wannan roba mai allura yana shiga achikin jikina. A chikin zuchiyata nake tambayar kaina, mike faruwa ne har ake karamin jini? Nanne nakali kane na wanda yaketa murna yana faman danna wayarsa domin yakira umma na yafada mata na farka amman ntwrk ya hanashi, kunsan network din 9ja da matsala... nache ahmad meyafaru dani ne akemin karin jini, budar bakinshi sai yache "yaya yusuf awarka ashirin da hudu kwanche anan, wannan itache leda ta ukku da akasanya maka" rufe bakinshi ne yayi dai dai da turo kofa da akayi,.... wani mutum ne mai matsai...

love sms

I count the hours, I count the days. How much I miss you, I count the ways. I miss your voice, I miss your touch. And I miss the face, That I love so much. How to describe it, There is now way. I walk around, In a permanent daze. I long to feel, Your warm embrace. And to see a smile, Upon your face. I will not sleep, Won't close one eye. Until you're home, Safe and alive. While you're overseas, And I'm safe at home. I think of you out there, In danger and alone. This is the life you've chosen, And I can't change your mind. You've found your inner bravery, And now I must find mine. I miss you so much, To the moon and the stars. And this feeling will go on, Until you're safe in my arms.

jega

Hukumar zaben Nigeria na can na gudanar da wani taro domin yanke hukunci akan ko za a gudanar da zaben kasa baki daya ranar asabar mai zuwa. Hukumar na ganawa ne da wakilan dukkanin jam'iyyun kasar domin yanke shawara. Wannan ganawa ta zo ne bayan ganawar da Majalissar Kasa ta yi ranar alhamis inda aka shafe awa bakwai ana tattaunawa akan batun zaben. Bayan da aka kammala taron wanda ya samu halartar tsaffin shugabannin Nigeria da gwamnoni da manya manyan jami'an tsaro, an shawarci hukumar zabe ta yi la'akari da halin da ake ciki na tsaro wajen yanke shawarar ranar da za a gudanar da zaben. Shugaban hukumar zaben dai ya gabatar da hujjojinsa na cewar a shirye hukumar ta ke ta yi zaben ranar 14 ga watan Febrairu Saidai wasu rahotanni na cewar manyan jami'an tsaro sun gabatar da kukan cewar ba zasu iya bayar da tabbascin tsaro ba idan aka ce za a yi zaben ranar asabar mai zuwa.

wata kisa

KISSA MAI TSORATARWA. Labarin wata mata da mijinta, tana tashinsa Sallar Asuba, wata rana sai ta tasheshi sai ya makara, jam'i ya tsere masa, sai ya samu wasu sukai jam'i na biyu, bayan sun idar, sai limamin masallacin yazo yace kaine mijin wance? Sai yace yaya akai kasan sunananta? Sai yace yau nayi mafarki duk wanda suka halarci jam'in farko sunzama yan Aljanna, sai naga harda mace guda daya, sai na tambaya sai akace matarkace, sai mijin ya tafi da sauri gida don yai mata bushara sai ya tarar tayi sujjada, Ranta ya koma ga mahaliccinsa.... Don haka idan ka kasance kana barci sanda kaso ka tashi sanda kaso, ba tareda kula da lokutan sallah ba, to tabbas zaka dauwama cikin bakin ciki...wallahi sallahce hutun duniya da lahira...Allah ya fada aharshen Annabi Ibrahim" Allah ka sanyani mai tsaida sallah nida zurriyata.... Suratu Ibrahim. To jamaa manufar kissa irin wannan tasa kowa ya duba yaga yaya yake da sallolin farilla, Allah kabamu ikon kiyayewa.

kuzo sha labari

GATANAN GATANANKU Wani manomi ne dai ya ke da jakinsa wanda ya ke aiki da shi shekara da shekaru. A kwana a tashi jaki ya fara tsufa har ba ya iya moriyar maigidansa da komai. Da manomi ya ga haka sai ya fara shawarar yadda zai rabu da jaki ko ma ya halaka shi ya huta da ciyar da shi da ya ke yi kullum. Da jaki ya gane abin da manomi ke shirin kulla masa sai ya gudu. Ya ce a ransa, "Bari na shiga birni na koyi waka, wata kila na zamo mai dogaro da kaina!" Yana cikin tafiya a hanya, sai ya hadu da kare yana kwance a gefen hanya, sai faman fuka ya ke yi. Jaki ya tambayi kare me ya same shi ya ke ta fuka? Kare ya ce, "Ai da kyar na sha a hannun mai gidana, wai zai kashe ni saboda yanzu na tsufa ba na iya farauto masa komai. Yanzu ina tunanin yadda zan yi da rayuwata in rika samun abinci" Jaki ya ce, "Af! Matsalarmu daya da kai. Ni zan shiga birni ne na koyi waka, idan za ka bi ni taso mu je." Kare ya tashi ya bi Jaki suka ci gaba da tafiya.Ba su yi nisa da ta...

hmm

Buhari Tsoron Jonathan yakeyi in ba hakaba ya fito ayi mukabalan dashi mana - Fani Kayode Darektan watsa labaran kamfen din Jonathan Fani Kayode yace tsoron mukabala da Jonathan Buhari yakeyi in ba haka ba me yasa yace bazaiyi mukabalan ba. Yace da ya fito su goga da Jonathan ya ga in Goodluck baiyi fatafata dashi ba. Kayode yace Buhari da Jam'iyyarsa na APC tsoron PDP da Jonathan sukeyi. Kun yarda dawannan korafi ko a'a?