Posts

Showing posts from June, 2018

DAREN LAILATUL-QADAR

Image
Daren LAILATUL QADR ya fi watanni dubu wanda ba wannan daren a cikinsa alheri, haka Qur’ani ya bayyana alherinsa ya fi na shekara tamanin da wata hudu. Hadisai sun zo suna bayanin samun wannan dare a cikin watan Ramadana ne. Sunna ta tabbatar kamar yadda Allah ya ce; • Kuma ana samunsa a cikin goman karshen Ramadan. • Ana samun wannan dare ne a cikin kwanukan mara, kamar daren 21,23,25,27,29, • Amma an fi sa ran samunsa a daren ashirin da bakwai (wato bayan an kai azumi na ashirin da shida). Amma hadisi ya zo MANZON ALLAH ( Salallahu Alaihi Wasallam ) yace “ku neme shi (daren lailatul qadr) a dare na mara”. An so mutum ya dage da ibada a cikin wannan daren ya raya sa da nau’o’in ibada, kamar karatun Alkur’ani da nafila da zikiri, hakanan ma an so mutum ya umurci iyalinsa da yin ibada a daren su dukkansu. • MANZON ALLAH (S alallahu Alaihi Wasallam)  ya ce wanda ya yi tsayuwar daren lailatul qadri Allah ya gafarta masa zunubansa wadanda suka gabata. ...

GA WASU HADISAN ANNABI S A W MASU MATUKAR MUHIMMANCI

*Mai yakai Hadisan Annibi Dadi?*  * HADISI NA FARKO *  Manzon Allah (S.A.W) ya na cewa Wanda ya karanta Qulhuwallahu Ahad kafa 10x Allah ya yi masa Alkawarin zai gina masa katafaren gida a gidan Aljanna. Sai Sayyidina Umar ya ce Ai to in haka ne sai mu dinga yawaitawa, sai Manzon Allah ya ce Allah shine mai yawaitawa Allah shine mai tsabtacewa.  * HADISI NA BIYU *  Manzon Allah ya na cewa duk wanda ya karanta suratul Kahfi a ranar jumaa Allah zai cika masa hasken sa har zuwa wata jumaa mai zuwa yana cikin haske yana cikin farin ciki. * HADISI NA UKU *  Annabi Muhammad (S.A.W) ya ce duk wanda ya haddace ayoyin goma na farkon kahfi Allah zai kiyaye shi daga fitinar Dujjal.  * HADISI NA HUDU *  Manzon Allah yana cewa Wanda ya karanta ayatul kursiyu bayan kowace Sallah ta farillah ba abinda zai hana shi shiga Aljanna sai in bai mutu ba.  * HADISI NA BIYAR *  Idan kazo zaka kwanta a shimfidar ka da daddare...