FALALAR KARANTA ALQUR’ANI MAI GIRMA

Image result for alqurani


FALALAR KARANTA ALQUR’ANI MAI GIRMA
1-      Hakika babu kokonto karatun Alqurani yana daga cikin mafifitan ayyuka sannan kuma yana daga cikin mafi girman abinda bawa zai nemi kusanci dashi zuwa ga ubangijinsa mai girma da daukaka.
An sharanta ga ko wane mumini da mumina da suyawaita karatun Alqurani mai girma ga namiji da mace babba da yaro an sharanta ga kowa da kowa dasu yawaita karantashi, saboda abinda ke cikinsa na alkairi mai girma da faida mai yawa kamar yadda Allah mai girma yace : HAKIKA WANNAN ALQURANI YANA SHIRYAWA ZUWA GA HANYA MAFI TSAYUWA KUMA YANA YIWA MUMINAI BUSHARA WADANDA SUKE YIN AIKI NA KWARAI HAKIKA SUNADA LADA MAI GIRMA: ALISRAU

2-      ALLAHU (SHN) yana cewa: KACESHI WANNAN ALQURANI SHIRIYANE KUMA WARAKANE GA WADANDA SUKAYI IMANI. FUSSULAT:44.

3-      Allahu madaukakin sarki yace inda yake yabon masu karanta Alqurani: HAKIKA WADANDA SUKE KARANTA LITTAFIN ALLAH SUKA TSAIDA SALLAH SUKA CIYAR DAGA ABINDA MUKA AZURTASU A FILI KO A BOYE SUNA KAUNAR KASUWANCI WANDA BABU HALAKA A CIKINSA. FADIR: 29
4-      MANZON ALLAH (S.A.W) yace: Kukaranta ayar Alqur’ani hakika zaizo ranar alkiyama yana mai ceton masu karantashi.

5-      Mai tsira da amincin Allah yace: mafi alkairin ku wanda ya karanta Al’qur’ani kuma ya karantar dashi.


6-      Manzon Allah yace: wanda yana tare da manyan mala’iku masu girma, wanda yake karanta Alqur’ani yake shan wahalar karantashi yana mai tsanani agareshi yana da lada biyu.

7-      Ko wanda harafin da musulmi ya karantashi daga cikin Al’qur’ani yana da lada, saboda karatun Alqur’ani yana shagaltar da mutum ga barin yi da mutune da annaminaci, Manzon Allah yace: wanda ya karanta harafi daga littafin Allah yanada ladan kyakykyawan aiki kuma kyakykyawan aiki yanada lada misalin goma. Ba ina cewa alif lamin harafi. A’a alif harafine, lam harafine, min harafine.


8-      Manzon Allah ya kasance wata rana azaune acikin sahabbansa yace: wanene daga cikinku zaiso ya fita zuwa (Badaha) yadawo da taguwa biyu manya batare  da zunubi ba, ko yanke zumunta? Sai suka ce muna son haka. Yace: dayanku yaje masallaci ya nemi sanin aya daya yafi abashi taguwa uku, ayoyi hudu sunfi masa taguwa hudu da kwatankwacin adadinsu na rakuma.

9-      Manzon Allah (S.A.W) yace: misalin mumininda yake karanta Alqur’ani kamar lemon tanjirin ne kamshinsa mai dadi dandanosa mai dadi, misalin muminin da baya karanta Alqur’ani kamar dabino bashi da kamshi dandanonsa mai zaki, misalin munafikin dayake karanta Alqur’ani kamar tazargade ce mai dadin dandanonta mai daci, misalin munafiki baya karanta Alqur’ani kamar gunace batada kamshi dandanonta mai daci.



10-    Abusa Zaburar wa ga karanta Alqur’ani mai girma yakamata ga abokai da tsaraiku su  dinga taruwa dan karantashi da yin darasunsa saboda falala mai girma dake cikin yin hakan, Manzon Allah (S.A.W) yana cewa: mutane basu taruba aikin daki daga dakunan Allah face sun karanta littafin Allah Sunayin darasunsa a tsakaninsu face sai nutsuwa ta sauka a garesu kuma rahama ta lullubesu kuma mala’iku sun kewayesu kuma Allah ya ambacesu acikin wanda suke wurusa. Sune (Mala’iku)    


don duba ko download na qura'ani mai fasarar Hasusa <a href="http://fm.nextwapblog.com/79556">Latsa nan</a>

Comments

Post a Comment

Popular posts from this blog

BAYANI AKAN JININ HAILA (JININ AL'ADA)

FARILLAN SALLAH

SUNAYEN SAHABBAN ANNABI (S.A.W) GUDA GOMA WA "YANDA SUKA MUTU DA CERTIFICATE NA SHIGA ALJANNAH