WASU DAGA CIKIN MU’UJIZOJIN ALKUR’ANI (1)
WASU DAGA
CIKIN MU’UJIZOJIN ALKUR’ANI (1)
Manzannin da Allah (SWT) Ya aiko tun
daga Annabi Nuhu (AS) zuwa kan Annabinmu Muhammad (SAW) kowa da irin baiwar da
Allah kan zaba Ya kebance shi da ita, don ya zamo darasi da kuma nuni ga mutanensa
cewa daga Allah yake. Amma kowane Manzo mu’ujizarsa tana shudewa ya zamo sai labarinta, amma ban da
Alkur’ani.
Ga misalai kamar haka:
- Annabi Sulaiman (AS) yana da mu’ujizozi masu yawa, daga ciki ya
yi magana da tsuntsaye har da tururuwa kamar yadda ya zo cikin Alkur’ani a Suratun Namli aya ta 17:
“Kuma aka tattaro wa Sulaiman rundunoninsa daga aljanu da mutane
da tsuntsaye, kuma aka kange su cikin ayari. Har lokacin da suka iso kan rafin tururuwa,
sai wata tururuwa ta ce, “Ya ku jama’ar tururuwa! Ku shiga gidajenku kada Sulaiman da rundunoninsa
su tattake ku, alhali ba su sani ba. Sai ya yi murmushi yana mai dariya daga
maganarta, kuma ya ce ya Ubangijina Ka cusa mini godiya ga ni’imarKa wadda ka ni’imta gare ni…” (27:17).
Haka kuma Annabi Sulaiman ya yi
magana da Alhuda-huda (wato daya daga cikin tsuntsayen da ke cikin ayarinsa)
kamar haka:
“Sai ya zauna ba da nisa ba (wato Alhuda-hudan) sannan ya ce, “Na san abin da ba ka sani ba, kuma na zo maka daga Saba’i da wani labara tabbatacce.” (27:22).
Bayan Annabi Sulaiman ya saurare shi
sai ya ce:
“Za mu duba, shin ka yi gaskiya ne ko
kuwa ka kasance daga makaryata, ka tafi da takardata wannan, sannan kuma ka
jefa ta zuwa gare su…”
(27:27-28).
- Annabi Musa (AS): Cikin mu’ujizozinsa yakan jefa sandarsa
ta zamo macijiya, ko ya saka tafin hannunsa a hammata ya fitar da shi yana
haske. Wannan magana ta tabbata a cikin Alkur’ani. Cikin Suratul Shu’ara’i, Allah Ya ce:
“Sai ya jefa sandarsa, sai ga ta ta zama kumurci bayyananne,
kuma ya fitar da hannunsa sai ga shi ya zama fari ga masu kallo.” (26:32-33).
- Annabi Isa (AS): Cikin nasa mu’ujizojin yakan rayar da matattu,
yana warkar da makaho da mai albaras da sauransu. Tabbacin hakan kuwa ya
zo alal misali cikin Suratu Ali Imrana kamar haka:
“Kuma (Ya saka shi) manzo zuwa Bani Isra’ila (yana mai cewa), “Lallai ne hakika na zo muku
da wata aya daga Ubangijinku, lallai ne ina halitta muku daga laka kamar siffar
tsuntsu, sannan in yi huri a cikinsa, sai ya kasance tsuntsu da izinin Allah,
kuma ina warkar da wanda aka haifa makaho da kuturu, kuma ina rayar da matattu,
da izinin Allah. Kuma ina fada muku abin da kuke ci da abin da kuke ajiyewa a
cikin gidajenku. Lallai ne a cikin wannan akwai aya a gare ku, idan kun kasance
masu yin imani.” (3:49).
- Annabi Muhammadu (SAW): Duk
wadannan kadan ke nan daga cikin mu’ujizozin da Allah Ya yi wa wasu daga cikin
Manzanni da AnnabawanSa. Sai dai wadannan manzanni littafin da aka aiko su
da shi ba shi ne mu’ujizarsu ba, amma Annabinmu Muhammadu (SAW), littafin
da aka aiko shi da shi zuwa gare mu shi ne mu’ujizarsa. Abin da yake cikin Alkur’ani ba ya tsufa, ko a ce yayinsa
ya wuce, kozamani ya bijiro da wani sabon abu da babu a cikin Alkur’ani. Alkur’ani littafi ne gagara-badau mai
cike da hikimomi da ilimin abubuwan da suka fi karfin a ce kirkirarsa aka
yi, ko a ce ba daga Allah yake ba. Cikinsa akwai umarni da hani da
tsoratarwa da bushara da gargadi da kwadaitarwa da ba da labarin abin da
ya wuce ko wanda ake ciki da lokaci mai zuwa. Ga shi da dadin sauraro da
saukin hadda da kuma saukin fahimtar ma’anarsa. Don haka Allah Ya kalubalanci dukkan masu
shakkar Alkur’ani a matakai da dama:
“Kuma, idan kun kasance a cikin shakka daga abin da Muka saukar
ga bawanMu, to ku zo da sura guda na daga misalinsa, kuma ku kirawo shaidunku
baicin Allah, idan kun kasance masu gaskiya.” (2:23).
“Ko suna cewa ya kirkiro shi ne? Ka ce to ku zo da sura guda
misalinsa, kuma ku kirayi duk wanda za ku iya kira bayan Allah, idan kun
kasance masu gaskiya.” (Suratu Yunus aya
ta 38).
“Ko suna cewa ya kirkiro shi ne? Ka ce sai ku zo da surori goma
misalinsa kirkirarru, kuma ku kirayi wanda kuke iyawa, baicin Allah idan kun
kasance masu gaskiya.” (Suratu Hud aya ta 13).
“Ka ce: “Lallai ne da mutane da aljanu za su
taru a kan su zo da misalin Alkur’ani, ba za su zo da misalinsa ba kuma ko da sashinsu ya
kasance mataimaki ga sashi.”
(17:88).
Wani abin dubawa shi ne, Annabi
Muhammadu (SAW) wanda shi aka saukar wa wannan littafi a
matsayin dan aiken Allah zuwa ga al’ummarsa, bai iya karatu da rubutu ba,
balle a ce shi ya kirkiro, ko ya ji daga maganganun magabata, ko masu ilimin zamaninsa
Allah (SWT) Ya ce:
“Kuma ba ka kasance kana karanta wani littafi ba gabaninsa, kuma
ba ka rubutunsa da hannuwanka, da ka yi hakan kuwa da masu barna sun yi shakka.” (Suratul Ankabut aya ta 48).
Shi Annabi Muhammad (SAW) bai yi yawo
ko’ina ba cikin fadin duniya, kafin
zuwan sakon Allah gare shi.Yana nan zaune cikin kasar da take sahara, amma Allah
Ya zabe shi Ya aiko masa da wannan littafi. Kuma Annabi (SAW) ba ya da wani
malami da za a ce daga wurinsa ya samu hikimar Alkur’ani. Allah (SWT) Yana cewa:
“Shin ba su kula da Alkur’ani, da ya kasance daga wanin
Allah ai da an samu saba wa juna mai yawa a cikinsa.” (4:82). Alkur’ani mai girma, saukarsa ta gabaci zamanin nan da muke ciki,
amma duk abin da ingantaccen ilimin kimiyyar zamani ya zo da shi tabbatacce, to
Alkur’ani ya rigaye shi. Wannan na daga cikin mu’ujizar Alkur’ani. Dubi misalai kamar haka:
1.
Ilimin
Halitta: Bayani a kan halittar dan Adam da dabbobi da tsirrai, wanda har yanzu
ake ta yin bincike a kansu. Game da halittar dan Adam, Allah (SWT) Ya ce a
cikin Suratul Muminun:
“Kuma lallai ne, hakika Mun halitta mutum daga wani tsantsa daga
laka, sannan Muka sanya shi digon maniyyi a cikin matabbata matsattsiya, sannan
Muka halitta shi gudan jini, sannan Muka halitta gudan tsoka, sannan Muka
halitta kasusuwa, sannan Muka tufatar da kasusuwan da wani nama, sannan Muka kaga
shi wata halitta daban….” (23:12,13,14).
Malam Aliyu Muhammad Sa’idu Gamawa
Comments
Post a Comment