Posts

Showing posts from January, 2017

WASU DAGA CIKIN MU’UJIZOJIN ALKUR’ANI (1)

Image
WASU DAGA CIKIN MU ’ UJIZOJIN ALKUR ’ ANI (1) Manzannin da Allah (SWT) Ya aiko tun daga Annabi Nuhu (AS) zuwa kan Annabinmu Muhammad (SAW) kowa da irin baiwar da Allah kan zaba Ya kebance shi da ita, don ya zamo darasi da kuma nuni ga mutanensa cewa daga Allah yake. Amma kowane Manzo mu ’ ujizarsa tana shudewa ya zamo sai labarinta, amma ban da Alkur ’ ani. Ga misalai kamar haka: Annabi Sulaiman (AS) yana da mu ’ ujizozi masu yawa, daga ciki ya yi magana da tsuntsaye har da tururuwa kamar yadda ya zo cikin Alkur ’ ani a Suratun Namli aya ta 17: “ Kuma aka tattaro wa Sulaiman rundunoninsa daga aljanu da mutane da tsuntsaye, kuma aka kange su cikin ayari. Har lokacin da suka iso kan rafin tururuwa, sai wata tururuwa ta ce, “ Ya ku jama ’ ar tururuwa! Ku shiga gidajenku kada Sulaiman da rundunoninsa su tattake ku, alhali ba su sani ba. Sai ya yi murmushi yana mai dariya daga maganarta, kuma ya ce ya Ubangijina Ka cusa mini godiya ga ni ’ imarKa wadda ka ni ’ imta g...

FINA FINAI GUDA GOMA MAFIYA KYAU NA KANNYWOOD A 2016

Image
A 2016 AN SAKI FIM MASU YAWA SOSSAI A KANNYWOOD. IDAN BA KU SAMU LOKACIN KALLON YAWANCIN FIM NA KANNYWOOD BA, MUN KAWO MUKU SHAWARA AKAN SHIRIN DA YA FI SHAʼAWA. Ƴan jaridar Arewa masu kula da wasan kwaikwayo sun lissafa bidiyo goma waɗanda sun fi daɗin kallo. Waɗanan fim sun ƙunshi salon wasa daban-daban kaman wasan soyyaya, wasa mai ban shaʼawa da kuma wasa mai ban dariya. 1. Afra Manyan Ƴan wasa cikin Afra su ne Adam A Zango, Fati Washa, Rabiu Rikadawa da Tijjani Faraga. Darektan wasa shi ne Nura M Inuwa. 2. Ahmad Cikin wannan shiri, akwai Ibrahim Maishunku, da Aminu Sheriff. Wannan wasa mai ban shaʼawa, ya shafi abubuwan da suka faru a yayin da an sace ɗiyar wani babban ɗan siyasa. Yakubu M Kumo shi ne marubucin wasa, kuma MuʼAzzam Idi Yari shi ne darekta. 3.Basaja Gidan Yari Idan kana shaʼawan wasan da ya shafi aikace-aikacen laifuka da bincike-binciken laifuka, ka ƙokarta ka kalla “Basaja Gidan Yari”. Babban Ɗan Wasan Kwaikwayo Adam A Zango s...

Makarantun Da ‘Ya’Yan Shugaba Buhari Suka Yi Da Shekarun Haihuwarsu

Image
Jaridar Premium Times ta wallafa wani sashe na littafin da wani farfesa a kasar Amurka, John Paden ya rubuta akan shugaban kasa Muhammadu Buhari mai suna ‘Muhammadu Buhari: The Challenges of Leadership in Nigeria’ inda suka zayyano makarantun da ‘yayan shugaban kasar suka yi daya bayan daya da shekarun da aka haife su. GA FASSARAR WALLAFAR: 1.  Fatima :  An haifi Fatima ranar 7 ga watan Maris, 1975. Ta yi makarantar firamari dinta a firamarin Sojojin Sama da ke Victoria Islands a jahar Lagos, ta yi karatun sakandaren ta a Kwalejin gwamnati dake Kaduna wato Government College, Kaduna; sannan ta yi digirin ta na farko a jami’ar Ahmadu Bello da ke Zaria kafin ta tafi kasar Ingila domin yin karatun babban digiri dinta a harkar kasuwanci. 2.   Nana-Hadiza :  An haifi Nana Hadiza a ranar 23 ga watan Yuni 1981. Ta fara  karatunta ne a Makarantar Essence International School da ke Kaduna sannan ta tafi Kasar Ingila domin Cigaba da karatunta. Ta yi Kar...