GIRMAN KAI KASHI NA SHABIYAR

GIRMAN KAI SABABINSA DA HADARINSA DA KUMA MAGANINSA.

Wallafar: Shaikh Abdulwahhāb Abdullah.

TAMBAYA TA 6:

Wane irin narko Ubangiji (swt) ya tanadawa ma su girman kai da ji-ji-da-kai da nuna taqama?

Ci gaba...

B) Uqubar da Allah ya ke yi wa masu girman kai a ranar lahira.

i) Allah yana wulaqantar da ma su girman kai a ranar Al-qiyama, domin hadisi ya tabbata daga Abu Hurairah (ra) ya ce: Manzon Allah (saw) ya ce: “Za a tashi ma su girman kai da ma su taqama ranar alqiyama, an mayar da halittarsu kamar qwayar komaiya, mutane su na tattaka su, saboda qasqancin su a gurin Allah.”

(Attawadu'u wal khumul na Ibn Abiddunya, Hadisi na 225)

ii) Qarshen makomar mai girman kai ita ce wuta:

Allah Madaukakin Sarki ya ce: “Lallai wadanda su ke girman kai ga barin bauta mini da sannu za su shiga Jahannama su na qasqantattu." - (Suratul Gafir aya ta 60).

A wata ayar kuma, Allah Madaukakin Sarki ya ce: “Za a ce: ku shiga qofofin Jahannama kuna ma su dauwama a cikinta. Tir da mazaunin masu girman kai.” - (Suratul Zummar aya ta 72).

Kuma hadisi ya tabbata daga Abdullahi Bin Mas’ud (ra) ya ce: Manzon Allah (saw) ya ce: “Duk wanda a zuciyarsa akwai girman kai gwargwadon qwayar komaiya, ba zai shiga Al-Jannah ba.” - (Sahihu Muslim: 91).

Kuma hadisi ya tabbata daga Abdullahi Bin Amr (ra) ya ce: Manzon Allah (saw) ya ce: “Duk wanda ya kasance akwai girman kai gwargwadon qwayar komaiya a zuciyarsa, Allah zai kifa shi akan fuskarsa a cikin wuta.” (Musnad Ahmad: 7015).

Wani hadisin kuma ya inganta daga Abu Hurairah (ra) daga Manzon Allah (saw) ya ce: Allah Madaukakin Sarki ya ce: “Jin girma mayafi na ne. Jin qasaita kwarjalle na ne. Duk wanda ya ja da ni a cikin daya daga cikinsu, zan jefa shi wuta." - (Sunan Abu Dawud:3567, Sunan Ibn Majah: 4164).

TAMBAYA TA 7:

Mene ne matsayi da kuma sakamakon da masu qanqan da kai su ke samu a gurin Allah?

AMSA:

Haqiqa hadisi ya tabbata daga Sauban (ra) ya ce: manzon Allah (saw) ya ce: “Duk wanda ransa ya bar gangar jikinsa (ya mutu), yana kubutacce daga abubuwa uku (3), zai shiga Al-Jannah; Girman kai da bashi (Ana nufin mai taurin bashi wanda ba shi da niyyar biya) da cin dukiyar baitul mali." - (musnad Ahmad: 22369. Sheikh Shuaib al-Arna'ux ya inganta shi).

A wani hadisin kuma Abu Hurairah (ra) ya ce: Manzon Allah (saw) ya ce: “Sadaka bata taba rage dukiya ba, kuma Allah bai taba qarawa bawansa mai yin afuwa ba sai buwaya, kuma ba wanda ya taba qanqan da kansa (tawalu'u) a cikinku face Allah ya daukaka shi." (Muslim: 4689).

Sai mun hadu a fitowa ta 16 da yardar Allah.

Comments

Popular posts from this blog

SUNAYEN SAHABBAN ANNABI (S.A.W) GUDA GOMA WA "YANDA SUKA MUTU DA CERTIFICATE NA SHIGA ALJANNAH

FARILLAN SALLAH

MTN BONANZA