HADISINMU NA YAU.
Abu Huraira (RA) yace: Watarana na tambayi Manzon Allah s.a.w cewa, “Ya Rasulillah, wanene acikin mutane zai fi kowa kasance wa acikin farinciki wanda zai fara samu samun ceton ka a ranar lahira?” sai Manzon Allah s.a.w yace, “Ya kai Abu Huraira, a tunani na babu wani mutum da zai Sake yi mini irin wannan tambayin bayan kai, saboda a yadda nake gani kai kadai ne mutum na farko da ya fara bayyana niyyar sa a fili zuwa ga hardace maganganu na. Mutum na farko mafi farinciki acikin mutane da zai fara samun cetona a ranar lahira shi ne mutumin da ya furta kalmar LA'ILAHA ILLALLAH da gaskiya har ya zuwa acikin zuciyar sa.” : Hadisin: Sahih Bukhari na 99. : Allahu Akbar Ya Allah kasa muna daga cikin ire- iren wadannan mutanen. Allah ka sada mu da rahamar ka a duniya da lahira.. @Ya Allah kasa mu dace da samun ceton Manzon ka, kuma Bawan ka Muhamadur Rasulullah )s.a.w( a ranar lahira..
Comments
Post a Comment