KA KARANTA ANATSE Labarin wani sarki. da masallaci

KA KARANTA ANATSE

!!! DARASI !!!

Wata rana wani sarki yayi niyyar gina qa'saitaccen Masallaci acikin garinsa

Tun ka'fin afara gini sarki yasa akasanar da mutanen garinsa cewa karda wani ko wata yataimaka da kud'i ko qarfi wajen gina wannan masallacin

sarki ne kawai zai gina wannan masallacin da kud'insa

koda mutanen gari sukaji haka sai kowa yaqi taimakawa da komai don gudun fushin sarki

Bayan an gina masallaci sai sarki yasa aka ka'wo wani qa'ton allo aka rubuta sunanshi ajiki sannan yasa aka maqala allon ajikin masallacin

don kowa yagane cewa sarki ne yagina wannan masallaci

Wata rana da dad dare sai sarki ya kwanta bacci

sarki yanacikin bacci ne sai yayi mafarkin

wani Mala'ika ya sauko daga sama yasauka akan masallacin

koda yasauka akan masallacin sai yagoge sunan sarki daga jikin allon nan da sarki yasa aka kafe ajikin masallaci
sannan yarubuta sunan wata matah

koda asuba tayi sai sarki yayi sauri yatura dogaransa suje suduba jikin masallaci sugani har yanzu akwai sunansa ajikin masalla'cin ko babu?

dogarai sukayi sauri sukaje sukaduba jikin masallaci sai sukaga

har yanyu sunan sarki na'nan ajikin allon da aka mane ajikin masallaci sai suka da'wo sukagayama sarki cewa haryanzu sunansa na nan ba agogeshi ba

da dare yayi sarki ya kwanta bacci sai yaqara yin mafarkin wannan mala'ikan yazo yagoge sunansa ya rubuta sunan wata matah

koda asuba tayi sai sarki yaqara tura dogaransa don suje suduba sugani shin har yanzu akwai sunansa ajikin masallacin?

dogarai sukaje sukaduba sukaga har yanzu sunan sarki na'nan ba agoge ba sai sukadawo sukagayawa sarki

arana ta 3 sai sarki yaqara mafarkin wannan mala'ikan yazo yagoge sunansa ya rubuta sunan wata matah

sai sarki yariqe sunan matar

koda asuba tayi sai sarki yaqara turawa aje agani shin har yanzu sunansa na'nan?

dogarai sukaje suka duba sukaga sunan sarki sai sukadawo suka gayamasa

bayan gari yayi haske ne sai sarki yagayama dogaransa sunan wannam matah yace suje sutaho da ita

dogarai sukaje sukataho da ita

sai sarki yacemata SHIN KE BAKIJI BANE CEWA NA HANA KOWA YA TAIMAKA MIN ACIKIN GININ WANNAN MASALLACIN?

sai matar tace ai naji kace kar kowa yataimaka maka don haka ne babu wanda yataimaka maka

ballantana ni danake tsohuwa kuma talakka

sarki ya kalleta yacemata KI GAYAMIN GASKIYA TSAKA'NINKI DA ALLAH

sai tsohuwar nan tace nidai ban taimaka da komai ba sai dai...

sarki yace: saidai me?

tsohuwa tace sai dai lokacin da akeyin ginin na biyo ta wajen sai naga wata dabba daga cikin dabbobin da suke kawo kata'ko da kayan ginin masallacin

ad'aure ajikin tirkenta

daga dukkanin ala'mu tagaji kuma tana'jin qishin ruwa

kuma ga ruwan akusa da ita amma bazata iya qa'risawa wajen ruwan ba sai namatsomata da ruwan sai tasha

koda sarki yaji haka sai
yace: wannan bayani naki ya nausar dani cewa

kinyi wannan aiki ne don Allah sai Allah s.w.t ya kar6i aikin ki

Ni kuma nagina masallaci don jama'a suce masallacin sarki

sai Allah s.w.t yaqi kar6ar aiki na.

sai sarki yayi umarni da aje agoge sunansa ajikin masalla'cin

sannan arubuta sunan wannan tsohuwar,

ya Allah s.w.t ga'mu muna masu tsarka ke niyya agare ka

YA ALLAH KA KAR6I AIKINMU,

Comments

Post a Comment

Popular posts from this blog

SUNAYEN SAHABBAN ANNABI (S.A.W) GUDA GOMA WA "YANDA SUKA MUTU DA CERTIFICATE NA SHIGA ALJANNAH

FARILLAN SALLAH

MTN BONANZA