HIKAYAR LAILA MAJNUN

Mun tsaya a inda Qais wanda ake yiwa lakabi da “Majnun lailah” yake bin kwararo kwararo da saman manyan duwatsu da bakin ruwa da cikin furanni yana rerawaLaila wadannan baituka masu motsa zuciya bai gusheba har saida akayi masa lakabi da “majnun wato (mahaukaci) !


Zanci gaba.


Duk dacewa itama Laila tana matukar son Qais wato (majnun) amma kuma hakan baya hanata ta wahalar dashi, a wasu lokutanma harda yi masa wulaqanci, bayan yin amfani da mallakeshi datayi wajen azabtar dashi, dama haka sha’anin mata yake shi yasa majnun acikin wani baiti nasa yace:


“Nace da wani babban malami da na gamu dashi a makka, dan Allah ka bani labarin wacce take cutar dani, azamanin da take jiji da kai (saboda ina sonta) shin hakan da take ba laifi bane ?”


Sai Malamin ya fadawa Qais cewa:


“Wallahi da sannu azaba zata shafe ta kuma a duniya ma saita hadu da bala’I.


Daganan Qai yace, saina kasa mallakar idona saida hawaye ya zubo cikin sauri yajiqa min aljihun rigata, sai nace, Allah yayafe mata laifinta duk da yake a duniya dan kadanne saboda son da nakeyi mata.


Qais ko Laila Majnun Bai gusheba a cikin wannan hali har saida yasami tabin hankali wato hauka.


Domin ya kasance idan yaga yara sunayin wasan kasa yakan zauna tare dasu yataro kasa ya rinqa gina gida irin wanda yara sukeyi da kasa yana cewa cikin waqa:


Abokaina kuzo kuga gidana nida laila”....!


A yayinda al-amari ya tsananta sai mutane suka baiwa mahaifin Majnun wato Qais shawara daya daukeshi ya kaishi ka’aba (dakin Allah) ya umarceshi daya roqi Allah ya cire masa son Laila!


Amma saboda tsananin soyayya a yayin da sukaje dakin ka’aba sai mahaifinsa yace masa:


kama tufafin ka’aba karoki Allah ya cire maka son Laila.


Sai Majnun yakama yace:


“Allah na tuba gareka daga dukkan laifi, amma bazan tuba daga son da nake yiwa Lailaba...


A taqaice haka majnun yarayu cikin wannan yanayi na abin tausayi !



Ita kuwa Laila tuni WIRD wanda ya aureta ya dauketa daga kasar Saudiyya gabaki daya zuwa kasar Iraqi.


Haka itama ta rayu cikin wannan mummunan yanayi abinka da ‘ya mace mai rauni saida rashin ganin Qais ya haddasa mata ciwon zuciya !


Daga nan itama takamu da ciwon zuciya saboda tsananin soyayyar da take yiwa Qais Majnun!


Tana cikin wannan haline na rashin ganin masoyinta Allah ya karbi rayuwarta!


A lokacin da Majnun yaji labarin rasuwarta saida yaje har kasar Iraqi yanemi inda take, da inda aka binne ta, a makabartar da aka binne laila a daidai gindin kabarinta yatare da zama.....!


Koda yaushe bashi da aiki sai kuka da wakokin soyayya a gareta.


Wata rana da safe sai masu wucewa suka hangoshi (Qais- wato Majnun) yakifa cikinsa akan qabarinta, koda akazo aka duba sai aka tarar Allah yayi masa cikawa!


Allahu akbar


Wannan shine Qarshen hikayar "LAILA MAJNUN" kunjifa yadda akeyin soyayya ruwa-ruwan ta.

Comments

  1. yusip@naij.com30 July 2015 at 06:02

    I lub u hussaina

    ReplyDelete
  2. Yusha'u yahaya abdulhameed31 May 2016 at 16:21

    Mungode matuka da fatan nasara ga masoya.

    ReplyDelete
  3. BILYAMINU YUSUF4 August 2016 at 16:59

    ya Allah kaba ni nima wadda nake so wato ziyada

    ReplyDelete
  4. Auwal abdullahi burji23 August 2016 at 14:23

    Ai nida lawanxalnah auwal mausa burji munyi tafi hakaa

    ReplyDelete
  5. ALLAH ya hada mu da masoyanmu

    ReplyDelete
  6. Rabiu Ibrahim Chigari26 September 2016 at 12:51

    @Aisha abba,
    Ameen

    ReplyDelete
  7. sulaiman sources9 October 2016 at 16:33

    allah yakarama son masu sammu

    ReplyDelete

Post a Comment

Popular posts from this blog

SUNAYEN SAHABBAN ANNABI (S.A.W) GUDA GOMA WA "YANDA SUKA MUTU DA CERTIFICATE NA SHIGA ALJANNAH

FARILLAN SALLAH

MTN BONANZA